Hukumar tara haraji ta jihar Kano (KIRS) ta sanar da wani gagarumin shiri na kara yawan kudaden shiga na jihar zuwa sama da Naira biliyan 100 nan da shekarar 2025.

 

Shugaban hukumar Dr. Zaid Abubakar ne ya bayyana hakan a yayin da hukumar ke bitar ayyukan hukumar na shekarar 2024 da kuma tsare-tsarenta na shekarar 2025.

 

A cewar Abubakar, KIRS ta bullo da tsare-tsare na matsakaita da kuma na dogon lokaci domin bunkasa kudaden shiga na jihar.

 

Shirin tara kudaden shiga na matsakaicin zango na nufin tara sama da Naira biliyan 100 a shekarar 2025, inda ake sa ran za ta haura Naira biliyan 200 a shekaru masu zuwa.

 

Musamman ma, gwamnatin jihar tace tana son su hado hancin naira biliyan 75 a shekarar 2025, amma KIRS ta kuduri aniyar wuce wannan buri.

 

Ya ce don cimma wannan manufa, KIRS na da niyyar yin amfani da fasaha a matsayin wani bangare na kokarin da ta ke yi na aiki da dabarun zamani.

 

 

“Hukumar tana shirin amfani da fasahar zamani ta ICT don tsarin sarrafa bayanai da haɓaka tattara kudaden shiga da bin diddigi da ci gaba, da kuma tabbatar da ingantaccen gudanarwa.”

 

“Gwamnatin jihar Kano kuma tana shirin sake duba dokokin samar da kudaden shiga na jihar domin karfafa kudaden shiga.”

 

 

Abubakar ya lura cewa gwamnan ya amince da sake duba wadannan dokoki, wanda ake sa ran kammalawa kafin karshen watanni 3 na farko na shekarar 2025.

 

Abdullahi Jalaluddeen Kano/WABABE

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Haraji a shekarar 2025 Naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Hezbollah, ta yi tir da Isra’ila kan kisan gillar da aka wani babban jigonta

Kungiyar Hezbollah, ta Lebanon ta yi tir da kakkausan lafazi da kisan da gillar da Isra’ila ta yi wani jigonta Sheikh Hussein Atoui, wanda ya yi shahada a ranar Talata, yayin wani hari da jiragen yakin Isra’ila a kusa da garin Damour na birnin Beirut.

Shugaban ofishin hulda da muslunci na kungiyar Hizbullah Sheikh Abdul Majid Ammar ya yi kakkausar suka dangane da kisan gillar dan gwagwarmayar, yana mai cewa abin takaici ne da makiya Isra’ila suka yi.

Sheikh Hussein Atoui shi ne shugaban Dakarun Al-Fajr, reshen Jamaa Islamiya (Kungiyar Musulunci) masu dauke da makamai, dake kawance da kungiyar Hamas.

Shugaban ofishin hulda da muslunci na kungiyar Hizbullah ya yi kira ga gwamnatin Lebanon da ta dauki matakai masu nagarta don kawo karshen ta’asar Isra’ila.

Babban jami’in kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon ya ce “Ya zama wajibi gwamnati ta wuce matsayin mai sa ido kawai, ta nisanci takaita kanta ga kalaman tofin Allah tsine ba tare da wani sakamako na hakika ba, sannan kuma ta dauki matakai masu tsanani, na gaggawa kuma masu tasiri a dukkan matakai da kuma hanyoyin da ake da su.”

A ‘yan watannin nan gwamnatin Isra’ila ta tsananta kashe-kashen da take yi a kasar Lebanon, inda ta karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma a watan Nuwamban bara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba ‘Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba – Gwamna Alia
  • Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara
  • Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON
  • Hezbollah, ta yi tir da Isra’ila kan kisan gillar da aka wani babban jigonta
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • Manchester United Na Zawarcin Matheus Cunha Na Wolves
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • Wang Yi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Sabon Ministan Harkokin Wajen Sudan Ta Kudu
  • Darajar Cinikin Sarin Kaya Da Sayen Kayan Masarufin Sin Ta Karu Da Dala Biliyan 452.5 a Rubu’In Farkon Bana
  • Sin Na Hasashen Samun Karin Yabanya A Shekarar 2025