Hukumar tara haraji ta jihar Kano (KIRS) ta sanar da wani gagarumin shiri na kara yawan kudaden shiga na jihar zuwa sama da Naira biliyan 100 nan da shekarar 2025.

 

Shugaban hukumar Dr. Zaid Abubakar ne ya bayyana hakan a yayin da hukumar ke bitar ayyukan hukumar na shekarar 2024 da kuma tsare-tsarenta na shekarar 2025.

 

A cewar Abubakar, KIRS ta bullo da tsare-tsare na matsakaita da kuma na dogon lokaci domin bunkasa kudaden shiga na jihar.

 

Shirin tara kudaden shiga na matsakaicin zango na nufin tara sama da Naira biliyan 100 a shekarar 2025, inda ake sa ran za ta haura Naira biliyan 200 a shekaru masu zuwa.

 

Musamman ma, gwamnatin jihar tace tana son su hado hancin naira biliyan 75 a shekarar 2025, amma KIRS ta kuduri aniyar wuce wannan buri.

 

Ya ce don cimma wannan manufa, KIRS na da niyyar yin amfani da fasaha a matsayin wani bangare na kokarin da ta ke yi na aiki da dabarun zamani.

 

 

“Hukumar tana shirin amfani da fasahar zamani ta ICT don tsarin sarrafa bayanai da haɓaka tattara kudaden shiga da bin diddigi da ci gaba, da kuma tabbatar da ingantaccen gudanarwa.”

 

“Gwamnatin jihar Kano kuma tana shirin sake duba dokokin samar da kudaden shiga na jihar domin karfafa kudaden shiga.”

 

 

Abubakar ya lura cewa gwamnan ya amince da sake duba wadannan dokoki, wanda ake sa ran kammalawa kafin karshen watanni 3 na farko na shekarar 2025.

 

Abdullahi Jalaluddeen Kano/WABABE

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Haraji a shekarar 2025 Naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Alakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Bisa Daidaito Tsakanin Sin Da Amurka Za Ta Amfanar Da Kamfanonin Duniya

Alakar tattalin arziki da cinikayya bisa daidaito da aminci kuma mai dorewa tsakanin Sin da Amurka ta dace da muhimman muradun kasashen biyu, kuma za ta amfanar da kamfanoni a duk duniya, a cewar mataimakin ministan cinikayya Wang Shouwen yayin wata ganawa da Ramon Laguarta, shugaban kamfanin PepsiCo a ranar Talata.

Da yake karin haske kan yadda kasar Sin ke da karfin gwiwar cimma burinta na bunkasa tattalin arzikinta na shekarar 2025 da aka gabatar a cikin rahoton aikin gwamnati, Wang, kuma wakilin harkokin cinikayya na kasa da kasa na kasar Sin, ya bayyana cewa, wasu jerin tsare-tsare da kasar ta bullo da su na fadada bukatun cikin gida, da sa kaimi ga inganta tsare-tsaren yin sayayya za su samar da karin damammaki ga kamfanonin masu jarin waje, ciki har da PepsiCo. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Hawan Daushe Na Sallar Bana
  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Hajjin Bana: Maniyata 3, 155 Suka Yi Rijista a Kano
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano
  • Ba Na Goyon Bayan Dakatar Da Gwamnan Jihar Ribas – Ndume
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara 
  • Alakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Bisa Daidaito Tsakanin Sin Da Amurka Za Ta Amfanar Da Kamfanonin Duniya
  • EFCC Ta Cafke Akanta-janar Na Jihar Bauchi Kan Zargin Badaƙalar Naira Biliyan 70