Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-14@18:31:47 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato Na Maraba Da Masu Zuba Jari

Published: 13th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Sakkwato Na Maraba Da Masu Zuba Jari

Gwamnatin jihar Sokoto ta ce tana kokarin samar da sauki da kuma tsarin zuba jari mai inganci wanda zai iya karfafa gwiwar masu zuba jari daga kasashen waje da na cikin gida zuwa jihar.

 

Wakilin Gwamnatin jiha kuma shugaban karamar hukumar Wamako Alh. Umar Ahmad Dundaye ya bayyana haka ne a wajen rabon magunguna da kamfanin siminti na BUA ke gabatarwa a kowace shekara ga asibitocin al’umma goma sha shida da ke yankin.

 

Ya ce gwamnatin jihar Sokoto tana karfafa duk masu zuba jari da ke da alaka kai tsaye ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar.

 

Ya ce gudunmawar BUA a fannin kiwon lafiya na jihar na daya daga cikin alfanun da jarin jihar ke samu.

 

Shugaban ya kara da cewa, a wani bangare na ayyukan da ya rataya a wuyan kamfanin, kamfanin yana kara habaka dimbin albarkatu wajen bunkasa al’ummomin da suka karbi bakuncinsa a karkashin karamar hukumar Wamako.

 

A nasa jawabin, Manajan Daraktan kamfanin simintin Alh. Yusuf Binji ya ce tallafawa al’ummomin da suka karbi bakuncinsu yana da matukar muhimmanci a wani yunkuri na kara kima ga zamantakewa da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin jama’ar yankin.

 

Nasir Malali/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta samar da ababen hawa ga shugabannin makarantun babbar  sakandare a fadin jihar.

Kwamishinan ilimi na jihar, Farfesa Isa Yusuf Chamo, ne ya bayyana hakan yayin wani taro da ya gudanar da shugabannin makarantu a garin Dutse.

A cewarsa, za a gyara gidajen ma’aikatan makarantun sakandare domin saukaka matsalar masauki ga malamai da sauran ma’aikata da ba malamai ba.

Farfesa Chamo, wanda Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Harkokin Ilimi, Malam Abdullahi Hudu, ya wakilta, ya ce taron ya na da nufin tattauna shirin dawowa  makarantu bayan hutun da aka yi a jihar.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ta sanya bangaren ilimi a sahun gaba saboda muhimmancinsa ga ci gaban jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa gwamnatin jihar ta dauki malamai 7,000 domin inganta tsarin koyarwa a makarantu, inda ya kara da cewa za a dauki ma’aikatan girki na J-Cook domin kara karfafa harkar gudanarwar makarantu.

A jawabansu daban-daban, wasu daga cikin Daraktoci da Shugabannin makarantu, sun bukaci a sake duba kudaden gudanar da makarantu, da samar da kwamfutoci da kayan aikinsu, da bayar da tallafi da kuma samar da malamai domin inganta ayyukan koyarwa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Siyo Tan Tan 360 Ga Manoma
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza