Gwamnatin Jihar Sakkwato Na Maraba Da Masu Zuba Jari
Published: 13th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Sokoto ta ce tana kokarin samar da sauki da kuma tsarin zuba jari mai inganci wanda zai iya karfafa gwiwar masu zuba jari daga kasashen waje da na cikin gida zuwa jihar.
Wakilin Gwamnatin jiha kuma shugaban karamar hukumar Wamako Alh. Umar Ahmad Dundaye ya bayyana haka ne a wajen rabon magunguna da kamfanin siminti na BUA ke gabatarwa a kowace shekara ga asibitocin al’umma goma sha shida da ke yankin.
Ya ce gwamnatin jihar Sokoto tana karfafa duk masu zuba jari da ke da alaka kai tsaye ga ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar.
Ya ce gudunmawar BUA a fannin kiwon lafiya na jihar na daya daga cikin alfanun da jarin jihar ke samu.
Shugaban ya kara da cewa, a wani bangare na ayyukan da ya rataya a wuyan kamfanin, kamfanin yana kara habaka dimbin albarkatu wajen bunkasa al’ummomin da suka karbi bakuncinsa a karkashin karamar hukumar Wamako.
A nasa jawabin, Manajan Daraktan kamfanin simintin Alh. Yusuf Binji ya ce tallafawa al’ummomin da suka karbi bakuncinsu yana da matukar muhimmanci a wani yunkuri na kara kima ga zamantakewa da zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin jama’ar yankin.
Nasir Malali/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Amince Da Biyan Bashin Albashin Ma’aikatan Tsaftar Muhalli 2,369
A cewarsa, amincewar wani gagarumin yunkuri ne na tallafawa dorewar tsafar muhalli a jihar.
Ya yaba da yadda jihar ke ci gaba da kokarin inganta rayuwar ‘yan jiharta da kuma tsaftar muhalli.