Jirage Marasa Matuƙa 140 Suka Kai Hari Cikin Dare A Ukraine
Published: 13th, February 2025 GMT
Rundunar sojin saman Ukraine, ta ce jirage marasa matuƙa 140 ne suka kai mata hare-hare cikin dare.
Hare-haren sun fi ƙamari a yankunan Odessa da Kharkiv, a cewar sojojin.
Rundunar sojin saman ta kuma ce ta samu nasarar kare wasu hare-haren daga ciki, yayin da ta tabbatar da kakkaɓo 85 daga cikin jiragen.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da manyan hafsoshin tsaron ƙasashen Nato ke taro a birnin Brussels, inda ake sa ran batun yaƙin Ukraine ne zai mamaye agjandar taron.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi
Wani matashi da aka kama kan yin gunduwa-gunduwa da budurwarsa da suka haɗu a Facebook bayan ta je ɗakinsa ya bayyana dalilinsa na aikata hakan.
Matashin mai shekaru 29 da ke iƙirarin malumtar addini ya amsa a wurin ’yan sanda masu bincike cewa shi ne ya yi wa gawar budurwar tasa gunduwa-gunduwa.
Ya shaida musu cewa a Facebook ya haɗu da ita, inda daga bisani ta ziyarci ɗakinsa a unguwar Olunlade a garin Ilori, bayan ta je wani biki.
Sai dai ya musanta zargin da ake masa na kashe ɗalibar mai suna Hafsah Yetunde Bello domin yin tsafi.
Jirgin soji ya kashe fararen hula a Katsina Malaman addini sun yi wa ’yan siyasa juyin mulki —Sule Lamiɗo Ku tona asirin ’yan tsubbu —Sarkin Ilori ga malaman addiniA cikin bidiyon tambayoyin da ’yan sanda ke wa matashin mai suna Abdulraham Bello, ya ce bayan zuwan budurwar tasa ne ya je ya sayo mata abinci, bayan ta bayyana masa cewa tana jin yunwa.
Ya shaida wa masu binciken nasa cewa bayan ya dawo daga sayo abincin ne ya iske ta tana shassheka a ɗakin.
“Ba a jima ba sai ta mutu. Ni kuma na tsotsa, babu wanda zan iya zuwa gaya wa ya taimaka min, shi ne ne sassara gawarta na yi mata gunduwa-gunduwa na je na jefar a wata bola a unguwar.
“A rikice nake, ban san abin da zan yi ba, ko tunanin wata hanya ta daban. Amma ban taɓa yin haka ba, wannan ne karon farko,” in ji matashin a ofishin ’yan sanda.
A cikin bidiyon da ya yi jawabin nasa cikin harshen Yarbanci ya bayyana cewa a halin yanzu yana neman gurbin karatu ne a Jami’ar Jihar Kwara (KWASU), Malete.
Mamaciyar dai ɗalibar aikin ƙarshe ce a Kwalejin Koyarwa ta Jihar Kwara.