Kungiyar Hamas Ta Bukaci Al’ummar Duniya Ta Goyi Bayan Al’ummar Falasdinu Kan Batun Neman Korarsu Daga Kasarsu
Published: 13th, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta yi kira ga ƙungiyoyin duniya da su fitar da matsayinsu a ranakun Juma’a da Asabar da kuma Lahadi don yin watsi da batun neman tilastawa Falasdinawa yin hijira daga Zirin Gaza
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yi kira ga al’ummar Falastinu, al’ummar Larabawa da al’ummar musulmi da dukkan ‘yantattun kasashe a duk fadin duniya da su fito domin gudanar da gagarumar zanga-zanga da tarukan goyon bayan al’ummar Falasdinu gami da hadin gwiwa a dukkanin birane da wuraren taruwar duniya, domin jaddada yin watsi da yin Allah wadai da shirin korar al’ummar Falastinu daga kasarsu ta gado.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a jiya Laraba ta ce: Ranakun Juma’a, Asabar da Lahadi masu zuwa su kasance wani yunkuri na duniya, inda ake za a daga muryoyi masu karfi domin nuna adawa shirin tilastawa Falasdinawa gudun hijira da korarsu daga muhallinsu, wanda ‘yan mamaya da magoya bayansu suke kiran a taimaka musu wajen cimma wannan mummunar manufa.
Hams ta jaddada cewa: Wannan zanga-zangar suna zuwa ne domin nuna goyon baya ga haƙƙin da al’ummar Falasdinawa suke da shi na kare ƙasarsu, daga ciki kuwa har da ‘yancinsu, ‘yancin kai, hakkin tsara makomarsu da kubutar da kasarsu daga hadamar ‘yan mamaya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila
Gwamnatin Isra’ila ta sanar da korar shugaban hukumar liken asiri ta cikin gidan kasar Ronen Bar, wanda Firaministan kassar Benjamin Netanyahu ya ce bai gamsu da kwarewarsa ba hasali ma ba’a yarda da shi.
“Gwamnati baki daya ta amince da shawarar Firaminista Benjamin Netanyahu na kawo karshen wa’adin” Ronen Bar, wanda zai bar ofis idan aka nada magajinsa ye zuwa ranar 10 ga watan Afrilu, in ji ofishin Firayim Minista a cikin wata sanarwa.
Rashin gamsuwa da aikin na kokaren shugaban hukumar ta Shin-bet, ta fito fili a baya bayan bayan bayannan da suke fitowa game da harin kungiyar Hamas na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.
Ronen Bar, wanda aka nada a watan Oktoba 2021 na wa’adin shekaru biyar, ya tabbatar tun kafin yanke hukuncin cewa zai kare kansa a gaban “hukumomin da suka dace”.
A cikin wata wasika da ya aikewa jama’a da yammacin Alhamis, ya bayyana cewa dalilan da suka sa aka kore shi daga aiki, wanda Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Lahadi, ya dogara ne da “sha’awar kansa” da nufin “hana bincike kan al’amuran da suka shafi harin ranar 7 ga Oktoba da wasu muhimman batutuwa da Shin Bet ke bincikar su.”
Dama shugaban hukumar ya amince kwanan baya da gazawar hukumar da ayek jagoranta wajen hana harin na Hamas.
A cikin wata sanarwa da aka fitar kwanan baya, shugaban hukumar ta Shin Bet, Ronen Bar, ya amince da cewa, hukumar ta ” gaza a cikin aikinta” na dakile ayyukan Operation Al-Aqsa, tare da kutsawa manyan sansanonin Isra’ila bayan da sojoji da ‘yan sandan gwamnatin suka yi kaca-kaca da su, kuma y ace ya dauki nauyin gazawar a wuyansa.
Hukumar ta amince da gagarumin gibi a cikin tattara bayanan sirri da kuma dogaro da matakan kariya da ake da su, wanda ya haifar da rashin fahimtar kungiyar Hamas, tare da sauran kungiyoyin gwagwarmaya.
Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wani “binciken cikin gida” ya nuna cewa, an gaza wajen dakile harin na Hamas.
Binciken da sojojin Isra’ila suka gudanar ya soki yadda gwamnatin kasar ke dogaro da bayanan sirri da kuma raina karfin Hamas, kura-kuran da suka haifar da mummunan sakamako ga gwamnatin Isra’ila.