Kungiyar Hamas Ta Bukaci Al’ummar Duniya Ta Goyi Bayan Al’ummar Falasdinu Kan Batun Neman Korarsu Daga Kasarsu
Published: 13th, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta yi kira ga ƙungiyoyin duniya da su fitar da matsayinsu a ranakun Juma’a da Asabar da kuma Lahadi don yin watsi da batun neman tilastawa Falasdinawa yin hijira daga Zirin Gaza
Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta yi kira ga al’ummar Falastinu, al’ummar Larabawa da al’ummar musulmi da dukkan ‘yantattun kasashe a duk fadin duniya da su fito domin gudanar da gagarumar zanga-zanga da tarukan goyon bayan al’ummar Falasdinu gami da hadin gwiwa a dukkanin birane da wuraren taruwar duniya, domin jaddada yin watsi da yin Allah wadai da shirin korar al’ummar Falastinu daga kasarsu ta gado.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a jiya Laraba ta ce: Ranakun Juma’a, Asabar da Lahadi masu zuwa su kasance wani yunkuri na duniya, inda ake za a daga muryoyi masu karfi domin nuna adawa shirin tilastawa Falasdinawa gudun hijira da korarsu daga muhallinsu, wanda ‘yan mamaya da magoya bayansu suke kiran a taimaka musu wajen cimma wannan mummunar manufa.
Hams ta jaddada cewa: Wannan zanga-zangar suna zuwa ne domin nuna goyon baya ga haƙƙin da al’ummar Falasdinawa suke da shi na kare ƙasarsu, daga ciki kuwa har da ‘yancinsu, ‘yancin kai, hakkin tsara makomarsu da kubutar da kasarsu daga hadamar ‘yan mamaya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Za Mu Kai Farmakin “ Wa’adus-Sadik” Na 3 Akan ‘Yan Mamaya
Mataimakin kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran “IRGC” ya sanar da cewa; Iran za ta kai farmakin “Wa’adus-Sadik 3” a lokacin da ya dace.
Laftanar janar Ali Fadwi ya kuma yi ishara da yakin Gaza, yana bayyana cewa, su kansu ‘yan sahayoniya sun bayyana cewa Hamas ta yi nasara, su kuma ba su cimma manufarsu ba.
Iran dai ta kai wa HKI hare-hare guda biyu a aka bai wa Sunan “ Wa’adussadik” na daya da na biyu. Hare-haren na Iran dai sun kasance mayar da martani ne akan harin da HKI ta kai wa karamin ofishin jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a kasar Syria da kuma kashe mata jami’an soja masu bayar da shawara ga gwamnatin Damascuss. Na biyun kuwa ya kasance mayar da martani akan kisan gillar da ‘yan sahayoniyar su ka kawo a Tehran wanda ya yi sanadiyyar shahadar shugaban kungiyar Hamas Shahid Isma’ila Haniyyah.
A wani gefen, shugaban kungiyar Hamas a yankin Gaza, Khalil Hayyah ya fada a makon da ya shude cewa; Iran ta kasance a sahun gaba wajen taimakawa gwgawarmayar Falasdinu, kuma muna da tabbacin cewa za ta cigaba da yin hakan.