Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta jaddada cewa: Al’ummar Iran ba zata taba amincewa da gudanar da duk wani zaman tattaunawa karkashin matsin lamba ba

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta mayar da martani ga yarjejeniyar tsaron kasa ta shugaban kasar Amurka, tana mai jaddada cewa: Iran ta yi watsi da duk wata tattaunawa karkashin matsin lamba, tana mai jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran bisa tsarinta na asali a ko da yaushe tana goyon bayan samar da hanyoyin diplomasiyya kan batutuwa daban-daban da suka hada da batun Shirin makamashin nukiliya, kuma tana goyon bayan warware al’amura ta hanyar diflomasiyya ciki har da batun Shirin makamashin nukiliyarta, sannan ta tabbatar da hakan a tsawon shekaru fiye da ashirin na yin riko da batun warware takaddamar shirinta na makamshin nukiliay.

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta fitar ya zo ne a matsayin mayar da martani ga yarjejeniyar tsaron kasa ta shugaban kasar Amurka da ta ce: A ranar 4 ga watan Fabrairun shekarar 2025 ne shugaban kasar Amurka ya rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaron kasa ta shugaban kasa, inda ya ba da umarnin sake farfado da manufar mafi girman matsin lamba kan al’ummar Iran. Gwamnatin Amurka ta yi ikirarin sake farfado da manufar matsin lamba, duk da cewa siyasarta ta baya ta takunkumin kan Iran bata daina aiki ba kuma a halin yanzu ta jaddada aniyarta ta kara tsananta matakan takunkumin kan Iran a wannan lokaci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar

Iran, ta yi Allah wadai da harin ta’addancin da ya yi sanadin mutuwar gomman mutane a wani masallaci a kudu maso yammacin Jamhuriyar Nijar.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Esmaeil Baghaei ya yi kakkausar suka kan harin da aka kai wa masallata.

Akalla mutane 44 ne suka mutu yayin da 13 suka jikkata a harin da aka kai a kauyen Fonbita da ke cikin kauyan Kokorou dake jihar Tillabery wanda ya faru a lokacin da wasu ‘yan ta’addan na kungiyar Da’ish a yankin Sahara (ISGS) suka far wa masallacin, inda suka auka wa masu ibada dake sallar Juma’a.

Baghaei ya bayyana cewa, wannan ta’addancin da aka aikata a lokacin sallar Juma’a ya saba wa ka’idar Musulunci, kuma ya saba wa dukkanin ka’idojin shari’a da hakkin dan Adam na kasa da kasa.

Kakakin na Iran ya jaddada muhimmancin kara inganta hadin gwiwa a matakai daban-daban na shiyya-shiyya da na kasa da kasa don dakile da yaki da ta’addanci.

Ya zama dole a gurfanar da masu hannu a harin ta’addanci da kuma hukunta su.

Baghaei ya nuna juyayi ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su da gwamnati da kuma al’ummar Nijar kan harin ta’addanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  • An yi wa wata karya tiyatar ceton rai
  • Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu