Tawagar Kasar Saudiyya Ta Kai Ziyarar Ta’aziyya Jihar Jigawa
Published: 13th, February 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya karbi bakuncin tawaga daga kasar Saudiyya karkashin jagorancin Sheikh Nuhu Idris Fallata shugaban hukumar Saudiyya mai kula da ciyar da Alhazai.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tawagar ta zo ne domin ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa da dansa ya rasa.
Sheikh Fallata ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu.
Tawagar ta kuma yabawa tare da karrama Gwamna Namadi bisa kulawa da jajircewarsa wajen kyautata rayuwar Alhazai.
A cewar tawagar, jihar Jigawa ta yi fice mai ban sha’awa a lokacin aikin Hajjin shekarar 2024.
Shi ma da yake nasa jawabin babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jiha Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yabawa tawagar bisa karrama gwamnan jihar ta Jigawa.
Wadanda suka raka tawagar sun hada da babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jiha, Alhaji Ahmed Umar Labbo, da daraktan ayyuka Alhaji Muhammad Garba, da Alhaji Isah Idris Gwaram da dai sauransu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Saudiyya Ta aziyya
এছাড়াও পড়ুন:
Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi
Sama da gidaje dari biyu da arba’in ne aka lalata a daren Talatar da ta gabata, ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shafe sa’o’i ana yi a unguwar Garin Kestu Atuwo dake karamar hukumar Shanga ta jihar Kebbi.
Da yake jajantawa wadanda abin ya shafa, Gwamna Nasir Idris ya shawarci gidajen da abin ya shafa da su dauki lamarin a matsayin wani kaddara daga Allah Ta’ala.
Shugaban karamar hukumar Shanga, Alhaji Audu Dan Audu, ya wakilce shi, ya ce ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a daren ranar Talata ya lalata gidaje da dukiyoyi na miliyoyin Naira, ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki ganin yadda ba a yi asarar rayuka ba.
Ya kuma yi kira gare su da su yi hakuri domin nan bada jimawa gwamnatin jihar za ta mika musu tallafi da suka hada da kayayyakin gini.
Abdullahi Tukur