Tawagar Kasar Saudiyya Ta Kai Ziyarar Ta’aziyya Jihar Jigawa
Published: 13th, February 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya karbi bakuncin tawaga daga kasar Saudiyya karkashin jagorancin Sheikh Nuhu Idris Fallata shugaban hukumar Saudiyya mai kula da ciyar da Alhazai.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tawagar ta zo ne domin ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa da dansa ya rasa.
Sheikh Fallata ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu.
Tawagar ta kuma yabawa tare da karrama Gwamna Namadi bisa kulawa da jajircewarsa wajen kyautata rayuwar Alhazai.
A cewar tawagar, jihar Jigawa ta yi fice mai ban sha’awa a lokacin aikin Hajjin shekarar 2024.
Shi ma da yake nasa jawabin babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jiha Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yabawa tawagar bisa karrama gwamnan jihar ta Jigawa.
Wadanda suka raka tawagar sun hada da babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jiha, Alhaji Ahmed Umar Labbo, da daraktan ayyuka Alhaji Muhammad Garba, da Alhaji Isah Idris Gwaram da dai sauransu.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Saudiyya Ta aziyya
এছাড়াও পড়ুন:
Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa
Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF), ta buƙaci Shugaba Bola Tinubu da gaggauta janye dakatarwar da ya yi wa Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, Mataimakiyarsa, da ’Yan Majalisar Dokokin jihar.
Da yake magana a madadin ƙungiyar, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya ce babu wani dalili da ya dace da zai sa shugaban ƙasa ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar.
Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a BenuweYa bayyana cewa, kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanadi ayyana dokar ta-ɓaci ne kawai a lokuta na matsanancin rikici kamar yaƙin basasa, ko rushewar doka da oda, wanda a cewarsa babu ɗaya daga cikinsu da ya faru a Jihar Ribas.
NEF, ta zargi Gwamnatin Tarayya da yin hakan ne saboda son rai, ba don amfanin al’umma ba.
Ƙungiyar ta yi zargin cewa rikicin siyasar yana da nasaba da taƙaddamar da ke tsakanin gwamnan da aka dakatar da tsohon gwamnan jihar wanda yanzu ministan Gwamnatin Tarayya ne.
Dattawan sun buƙaci gwamnati da ta dawo da dimokuraɗiyya, adalci, da zaman lafiya a Jihar Ribas.
Haka kuma, sun gargaɗi Gwamnatin Tarayya da kada ta bari irin wannan rikicin siyasa ya tsananta a wasu jihohi kamar Kano, inda ake ci gaba da samun saɓani dangane da masarautar Kano.