Shugaban kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Son Shiga Yaki Amma Tana Shirye Wajen Fuskantar Barazana
Published: 13th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Ba su neman yin yaki, amma ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen fuskantar duk wata barazana
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Iran ba za ta mika kai ga duk wata barazana ba, kuma ba za ta ja da baya ba wajen fuskantar matsin lamba, yana mai jaddada cewa; Kasarsa ba ta neman yaki da wata kasa, sai dai tana kokarin karfafa dangantakar abokantaka da kasashen makwabta.
Shugaban ya bayyana hakan ne a yayin ziyarar da ya kai lardin Bushahar inda ya gana da al’umma tare da jinjinawa sadaukarwar shahidai musamman shahidan wannan lardin, a daidai lokacin da ake cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci, yana mai jaddada aniyarsa ta bin diddigin matsalolin lardin tare da ministoci da jami’an da abin ya shafa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas Ta Ce Tana Iya Sakin Dukkan Fursinonin Yahudawa Gaba Daya A Lokaci Guda
Kungiya mai gwagwarmaya ta Falasdinawa Hamasa ta bayyana cewa tana iya sakin fursinoni yahudawa wadanda suke hannunta gaba daya a lokaci guda a marhala ta biyu ta musayar fursinoni tsakaninta da tare da sharadin ta cika al-kawulan da ta nauyi alhakin aiwatar da shi a wannan karon. Daga cikin har da maida tsagaita wutan na din din din
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Taher Al-Nounou ya cewa idan an yi haka za’a kammala musayar fursononin gaba daya, sannan HKI ta sake duk fursinonin falasdinawa gaba daya da suke hannunta. Yin hakan ya na nuna yanda al-amarin musayar Fursinoni yake da muhimmancin ga falasdinawa.
Kafin wannan sanarwan dai ministan yaki na HKI Isarael Katz ya bayyana cewa HKI tana shirin shiga tattaunawa ba gaba ba kai tsaye ba, da Falasdinawa a marhala ta biyu da kungiyar Hamas, Ya kuma kara da cewa gwamnatinsa tana samun goyon bayan gwamnatin Amurka.
A zagaye na farko an musayar dai yahudawa 33 Hamas ta saka sannan Falasdinawa kimani 2000 suka sami yanci. Dakarun Qassam kadai ta saki yahudawa 19 a yayinda sauran kuma sauran kungiyoyin kuma sake sauran. A taunawa ta gaba ce za ta fayyace yadda tattaunawa ta gaba zata kasance.