Leadership News Hausa:
2025-03-28@18:54:28 GMT

Abin Da Ya Kamata Ku Sani Kan Wasan Roma Da FC Porto 

Published: 13th, February 2025 GMT

Abin Da Ya Kamata Ku Sani Kan Wasan Roma Da FC Porto 

Yan wasa 11 na farko da Fc Porto za ta yi zubi dasu:

Svilar, Mancini, Hummels, Ndika, Saelemaekers, Kone, Paredes, Angelino, Dybala, Pisilli, Dovbyk

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya bayar da gudummawar Naira miliyan 27 da buhunan shinkafa 300 ga mutanen da gobara ta shafa a ƙananan hukumomi uku da ke mazaɓarsa a Jihar Yobe.

Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Machina, Nguru, da Yusufari.

An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu

Sanata Lawan, ya jajanta wa mutanen da suka yi asarar dukiya sakamakon gobarar.

Ya ce haƙƙinsu ne su taimaka wa juna, kuma zai ci gaba da ƙoƙari don ganin cewa wadanda abin ya shafa sun samu tallafin da ya dace.

Ya bayyana cewa wannan tallafin zai ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da gwamnatin jihar ke yi na samar da agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa, tare da taimaka musu, su farfaɗo daga ɓarnar da gobarar ta yi musu.

A cewarsa, an ware Naira miliyan 12 da buhunan shinkafa 150 ga Ƙaramar Hukumar Machina, wanda za a raba a garuruwan Ngabarawa, Dole, Ghana, da Damai.

Ƙaramar Hukumar Nguru, za ta karɓi Naira miliyan biyar da buhunan shinkafa 50, wanda za a raba wa al’ummar Askema da Mirba.

Ƙaramar Hukumar Yusufari, za ta samu Naira miliyan 10 da buhunan shinkafa 100, wanda za a raba wa mutanen Tulo-Tulo da Isufuri.

Sanata Lawan, ya buƙaci gidauniyar SAIL Foundation, wacce ke kula da rabon tallafin, da ta tabbatar da gaskiya da adalci wajen raba wa waɗanda suka cancanta.

Ya kuma yi addu’a Allah Ya ba waɗanda abin ya shafa ikon jure wannan jarabta da sauƙi a gare su, musamman a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barcelona za ta yi asarar maki saboda saɓa dokar FIFA a wasanta da Osasuna
  • Kwankwaso Ya Yi Allah-wadai Da Kisan ‘Yan Arewa A Edo, Ya Buƙaci A Yi Adalci
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Musulmi Su Yi Kafin Da Kuma Ranar Sallah
  • Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Faransa
  • Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara
  • Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe
  • Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku