Mutanen Najeriya suna  bayyana fushinsu akan kara kudaden sayen cajin shiga kafar sadarwa na Internet –Data- da manyan kamfanoni irin su MTN da Airtel su ka yi, saboda yadda ake fama da matsalar rayuwa.

Kamfanin MTN shi ne mafi girma a tsakanin kamfanonin samar da hidimomi na hanyar sadarwa, inda a yanzu ake sayar da Giga 15, akan Naira 6,000 bayan da a baya take naira 2,000 ( wato daga dala 1.

33-3.99) da hakan yake nufin cewa an rubanya farashin sau uku.

Shi ma kamfanin Airtel ya kara yawan kudaden cajin nashi da kaso mai yawa.

Wannan Karin da kamfanonin su ka yi, ya bakanta ran masu amfani da su, musamman a wannan lokacin da ake fama da yanayi mai tsanani na  tattalin arziki.

Kamfanin MTN ya wallafa sanarwa a shafinsa na X cewa; Karin kudin ya zama wajibi domin gabatar da hidimomi  masu nagarta ga kwastomominsa, tare da neman gafara ga abokan hulda.

Wani daga cikin masu tofa albarkacin baki akan Karin na MNT; ya walllafa cewa; Rubanya kudi har sau uku? Lallai karshen duniya ya zo.”

Ana hasashen cewa Karin da aka yi zai shafi kananan ‘yan kasuwa da suke dogaro da hanyoyin sadarwar masu saukin kudi domin tafiyar da harkokinsu.

Ya zuwa yanzu dai kamfanin Globacom, da shi ne kamfani na uku mafi grima a cikin kasar, bai yi  Karin kudin ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya

Jaridar Ma’ariv ta Isra’ila ta bayyana adadin wadanda suka jikkata a cikin sojojin mamayar Isra’ila da kuma miliyoyin yahudawan sahayoniyya da suka samu matsalar tabin hankali a lokacin yakin Gaza

Jaridar “Ma’ariv” ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta bayyana a jiya litinin, adadin wadanda suka mutu a cikin jerin sojojin mamayar Isra’ila a yayin mummunan ayyukan ta’addancin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar kan Zirin Gaza, wanda ya shafe tsawon watanni 15 kafin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da musayar fursunoni a watan Janairun da ya gabata.

A cewar jaridar, sojoji 15,000 da ke cikin sojojin mamayar Isra’ila suka jikkata tun farkon yakin ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023, yayin da wasu 846 suka sheka lahira.

Daga cikin wadanda suka samu raunuka, sojoji 8,600 ne suka sami raunuka daban-daban na jiki, yayin da wasu 7,500 suka samu matsalolin tabin kwakwalluwa ciki har da firgita, damuwa, tashin hankali, rikirkicewar tunani, kamar yadda jaridar ta nakalto daga sashin  kula da dabi’ar ma’aikata da ke karkashin Ma’aikatar yakin haramtacciyar kasar Isra’ila.

Kanun labarai

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Kissoshin Rayuwa. Sirar Imam Alhassan (a) 19
  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • IRGC: Za Mu Kai Farmakin “ Wa’adus-Sadik” Na 3 Akan ‘Yan Mamaya
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • FG Ta Jaddada Bukatar Samarda Sabbin Ka’idojin Visa Domin Taimakawa Kasuwancin A Duniya
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Tituna Akan Kudi Naira Biliyan 6.3