HausaTv:
2025-03-23@03:32:58 GMT

Hamas: Za A Yi Musayar Fursunoni Kamar Yadda Aka Tsara

Published: 13th, February 2025 GMT

Kungiyar gwgawarmayar musulunci ta Hamas ta sanar da cewa, za a ci gaba da musayar fursunoni kamar yadda aka tsara a karkashin yarjejeniyar da aka cimmawa.

A yau Alhamis ne dai kungiyar ta Hamas ta sanar da  cewa za ta saki fursunoni kamar yadda yake a jadawalin da aka tsara.

Tashar talabijin din Aljazira ta ambato majiyar kungiyar ta Hamas tana cewa, tawagarta tana tattaunawa d a Masar da Katar  a matsayinsu na masu shiga tsakani musamman akan yadda za a kai wa mutanen Gaza, hadaddun matsugunan da za su rayu a ciki da kuma magunguna da sauran bukatu na  kiwon lafiya na gaggawa.

Haka nan kuma an warware matsalar kai kayan agaji da za a bari su rika shiga cikin Gaza ba tare da kakkautawa ba.

Wasu daga cikin matsalolin da aka warware sun hada bayar da damar shigar da manyan kayan aiki da motocin buldoza na kwace baraguzai, da makamashi, da kuma  magunguna.

Sanarwar da kungiyar ta Hamas ta wallafa a shafinta na “Telegram” ta ambato masu shiga tsakani da su ne kasashen Masar da Katar suna cewa, za su sa ido domin ganin cewa ana aiki da abubuwan da aka yi yarjejeniyar akansu.

Wannan matakin na kungiyar Hamas, ya zo ne bayan da a kwanaki kadan da su ka gabata ta sanar da dakatar da batun sakin fursunonin har illa masha Allah, saboda yadda HKI take take sharuddan yarjeniyar da aka cimmawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila

Gwamnatin Isra’ila ta sanar da korar shugaban hukumar liken asiri ta cikin gidan kasar Ronen Bar, wanda Firaministan kassar Benjamin Netanyahu ya ce bai gamsu da kwarewarsa ba hasali ma ba’a yarda da shi.

 “Gwamnati baki daya ta amince da shawarar Firaminista Benjamin Netanyahu na kawo karshen wa’adin” Ronen Bar, wanda zai bar ofis idan aka nada magajinsa ye zuwa ranar 10 ga watan Afrilu, in ji ofishin Firayim Minista a cikin wata sanarwa.

Rashin gamsuwa da aikin na kokaren shugaban hukumar ta Shin-bet, ta fito fili a baya bayan bayan bayannan da suke fitowa game da harin kungiyar Hamas na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

Ronen Bar, wanda aka nada a watan Oktoba 2021 na wa’adin shekaru biyar, ya tabbatar tun kafin yanke hukuncin cewa zai kare kansa a gaban “hukumomin da suka dace”.

A cikin wata wasika da ya aikewa jama’a da yammacin Alhamis, ya bayyana cewa dalilan da suka sa aka kore shi daga aiki, wanda Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Lahadi, ya dogara ne da “sha’awar kansa” da nufin “hana bincike kan al’amuran da suka shafi harin ranar 7 ga Oktoba da wasu muhimman batutuwa da Shin Bet ke bincikar su.”

Dama shugaban hukumar ya amince kwanan baya da gazawar hukumar da ayek jagoranta wajen hana harin na Hamas.

A cikin wata sanarwa da aka fitar kwanan baya, shugaban hukumar ta Shin Bet, Ronen Bar, ya amince da cewa, hukumar ta ” gaza a cikin aikinta” na dakile ayyukan Operation Al-Aqsa, tare da kutsawa manyan sansanonin Isra’ila bayan da sojoji da ‘yan sandan gwamnatin suka yi kaca-kaca da su, kuma y ace ya dauki nauyin gazawar a wuyansa.

Hukumar ta amince da gagarumin gibi a cikin tattara bayanan sirri da kuma dogaro da matakan kariya da ake da su, wanda ya haifar da rashin fahimtar kungiyar Hamas, tare da sauran kungiyoyin gwagwarmaya.

Wannan na zuwa ne kwanaki bayan wani “binciken cikin gida” ya nuna cewa, an gaza wajen dakile harin na Hamas.

Binciken da sojojin Isra’ila suka gudanar ya soki yadda gwamnatin kasar ke dogaro da bayanan sirri da kuma raina karfin Hamas, kura-kuran da suka haifar da mummunan sakamako ga gwamnatin Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa
  • An Rantsar Da Sabuwar Shugabar Kasar Namibia
  • Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila
  • Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas
  • ‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’
  • Kungiyar Hamas Ta Ce Falasdinawa Ba Za Su Bar Kasarsu Ba, Ko Da Son Ransu Ko Da Karfi