A takardar, wadda mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Rabi’u Ibrahim, ya sa wa hannu, Idris ya ce: “Rediyo ko yaushe hanya ce ta samun ingantaccen bayani kuma abin dogaro ne ga al’umma, musamman a lokutan da ake fuskantar matsaloli.

 

“A ‘yan shekarun nan, rediyo ya taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan jama’a kan sauyin yanayi da tasirin sa ga duniyar mu.

Tare da faɗin isar sa da sauƙin samun sa, rediyo yana da ikon ilimantarwa da ƙarfafa mutane su ɗauki matakan da suka dace don yaƙi da sauyin yanayi.”

 

Idris ya ambato jawabin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a taron COP29 na Majalisar Ɗinkin Duniya kan Sauyin Yanayi wanda aka gudanar a birnin Baku na ƙasar Azerbaijan inda Shugaban Ƙasar ya yi bayanin yadda Nijeriya take fama da matsalar sauyin yanayi da matakan da gwamnati ke ɗauka don rage fitar da hayaƙin da ke dagula yanayi, ƙarfafa juriya, da shigar da hanyoyin magance matsalar cikin tsare-tsaren ƙasa.

 

Idris ya yi kira ga gidajen rediyo a Nijeriya da su gabatar da shiryayyun bayanai da ilimantarwa kan sauyin yanayi, su haɗa kai da masana, da kuma tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin isar da ingantattun bayanai ga jama’a.

 

Ya ce: “Ta hanyar shirye-shiryen ilimantarwa da bayanai, za mu iya bai wa al’umma ilimi da kayan aiki da za su taimaka masu wajen daidaita kan su da sauyin yanayi da kuma rage tasirin sa.

 

“Haka nan, yana da matuƙar muhimmanci ga gidajen rediyo su haɗa kai da ƙungiyoyi da masana a fannin sauyin yanayi don samar da ingantattun bayanai ga masu sauraro.

 

“Ta hanyar tattaunawa da masana kimiyya, da ƙwararru a fannin muhalli, da masu tsara manufofi, za mu ƙarfafa fahimtar mu game da wannan matsala tare da nemo hanyoyin magance ta, bisa la’akari da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”

 

Ministan ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su duba halayen su na yau da kullum da kuma yin ƙananan canje-canje domin yaƙi da sauyin yanayi, kamar rage amfani da robobi, rage amfani da makamashi ko wutar lantarki, da haɓaka noma mai ɗorewa.

 

Har ila yau, ya jaddada cewa matsalar sauyin yanayi ba ta tsaya a wata ƙasa kaɗai ba kuma tana buƙatar haɗin gwiwar ƙasashe daban-daban don samar da mafita mai ɗorewa.

 

Yayin da yake taya UNESCO murna bisa ƙirƙirar Ranar Rediyo ta Duniya, Idris ya tabbatar da cewa gwamnati tana da niyyar amfani da rediyo don kawo sauyi mai kyau a cikin al’umma.

 

Ya ce: “Mu yi amfani da ƙarfin rediyo don kawo sauyi mai kyau a cikin al’ummomin mu da kuma yaƙi da mummunan tasirin sauyin yanayi.

 

“Ta hanyar haɗin gwiwa da himma tare, za mu iya gina Nijeriya mai ɗorewa da juriya.

 

“A wannan rana ta Ranar Rediyo ta Duniya, mu yi alƙawarin kawo sauyi da kare duniyar mu domin amfanin zuriyar da ke tafe.”

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a kan sauyin yanayi

এছাড়াও পড়ুন:

Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro

Wata mata mai suna Jennifer Castro ta shigar da ƙarar kamfanin jiragen sama na GOL da wata fasinja a kotu bisa wani faifan bidiyo aka wallafa da yake nuna matar ta ki barin kujerarta da ke kusa da taga saboda wani yaro da yake kuka.

Matar ’yar ƙasar Brazil da ta ƙi barin kujerar kusa da taga saboda wani yaro mai kuka ta shigar da ƙara a kotu.

Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato

Jennifer Castro, mai shekara 29 na daukar matakin shari’a a kan kamfanin jiragin sama na GOl da kuma fasinjar da ta ɗauki bidiyonta a lokacin da lamarin ya faru.

Lamarin wanda aka yi ta yadawa ta intanet, ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.

A cewar jaridar The New York Post, Castro na tuhumar kamfanin jirgin da kuma matar da ya nadi musayar takaddamar da suka yi, inda ta nemi diyya kan halin kunci da barnar da lamarin ya haifar mata.

Ta bayyana cewa, matakin da ta ɗauka na shigar da ƙarar shi ne don hana afkuwar irin wannan abin kunya ga jama’a a nan gaba.

Al’amarin ya ja hankalin jama’a saboda yada lamarin a kafafen sada zumunta.

Da take bayani a kan shari’ar, Castro ta ki bayyana adadin diyyar da take nema.

Ta ce, tana son hana irin wannan tozarta jama’a da abin da ta kira fallasa ba tare da izini ba a nan gaba.

Hakan na zuwa ne bayan da aka bayar da rahoton cewa, a watan da ya gabata ta fara “tunanin” daukar matakin shari’a.

Castro ta bayyana cewa, “tun bayan faruwar wannan lamarin, rayuwata ta shiga wani yanayi da ban taba tunanin sa ba.”

“Abin da ya kamata ya kasance kawai jirgin zirgazirgar na yau da kullun ya sauya zuwa wani abun kunya, yana fallasa ni da rashin adalci da haifar da sakamakon da ya shafi rayuwata ta sirri da ta sana’a.

Ni ce ake so na yanke hukunci a kan takaddama da hasashen mutanen da ba su ma san cikakken labarin ba.”

Castro ta ce lamarin ya fara ne a lokacin da take hawa jirgi, sai ta hangi wani yaro a zaune a lambar kujerar da ya kamata ta zauna.

Tunda ta riga ta zabi wurin zama na kusa da taga, Castro ta yi tsammanin yaron zai koma wani wurin zaman na daban.

“Na jira shi yadda ya kamata, amma ya kwantar da kansa a wata kujerar, sannan sai na zauna a kujerata ,” in ji ta.

Lamarin ya ta’azzara lokacin da wata ta fara daukar bidiyon Castro ba tare da izininta ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno
  • 2027: Masu Shirin Yin Kawance Na Duba Yiwuwar Zakulo Dan Takarar Da Zai Yi Wa’adi Daya
  • Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi
  • Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
  • An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe
  • Ku Kyautata Rayuwar Jama’a Ba Taku Ba — Buhari Ga Gwamnonin APC