A takardar, wadda mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Rabi’u Ibrahim, ya sa wa hannu, Idris ya ce: “Rediyo ko yaushe hanya ce ta samun ingantaccen bayani kuma abin dogaro ne ga al’umma, musamman a lokutan da ake fuskantar matsaloli.

 

“A ‘yan shekarun nan, rediyo ya taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan jama’a kan sauyin yanayi da tasirin sa ga duniyar mu.

Tare da faɗin isar sa da sauƙin samun sa, rediyo yana da ikon ilimantarwa da ƙarfafa mutane su ɗauki matakan da suka dace don yaƙi da sauyin yanayi.”

 

Idris ya ambato jawabin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a taron COP29 na Majalisar Ɗinkin Duniya kan Sauyin Yanayi wanda aka gudanar a birnin Baku na ƙasar Azerbaijan inda Shugaban Ƙasar ya yi bayanin yadda Nijeriya take fama da matsalar sauyin yanayi da matakan da gwamnati ke ɗauka don rage fitar da hayaƙin da ke dagula yanayi, ƙarfafa juriya, da shigar da hanyoyin magance matsalar cikin tsare-tsaren ƙasa.

 

Idris ya yi kira ga gidajen rediyo a Nijeriya da su gabatar da shiryayyun bayanai da ilimantarwa kan sauyin yanayi, su haɗa kai da masana, da kuma tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin isar da ingantattun bayanai ga jama’a.

 

Ya ce: “Ta hanyar shirye-shiryen ilimantarwa da bayanai, za mu iya bai wa al’umma ilimi da kayan aiki da za su taimaka masu wajen daidaita kan su da sauyin yanayi da kuma rage tasirin sa.

 

“Haka nan, yana da matuƙar muhimmanci ga gidajen rediyo su haɗa kai da ƙungiyoyi da masana a fannin sauyin yanayi don samar da ingantattun bayanai ga masu sauraro.

 

“Ta hanyar tattaunawa da masana kimiyya, da ƙwararru a fannin muhalli, da masu tsara manufofi, za mu ƙarfafa fahimtar mu game da wannan matsala tare da nemo hanyoyin magance ta, bisa la’akari da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”

 

Ministan ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su duba halayen su na yau da kullum da kuma yin ƙananan canje-canje domin yaƙi da sauyin yanayi, kamar rage amfani da robobi, rage amfani da makamashi ko wutar lantarki, da haɓaka noma mai ɗorewa.

 

Har ila yau, ya jaddada cewa matsalar sauyin yanayi ba ta tsaya a wata ƙasa kaɗai ba kuma tana buƙatar haɗin gwiwar ƙasashe daban-daban don samar da mafita mai ɗorewa.

 

Yayin da yake taya UNESCO murna bisa ƙirƙirar Ranar Rediyo ta Duniya, Idris ya tabbatar da cewa gwamnati tana da niyyar amfani da rediyo don kawo sauyi mai kyau a cikin al’umma.

 

Ya ce: “Mu yi amfani da ƙarfin rediyo don kawo sauyi mai kyau a cikin al’ummomin mu da kuma yaƙi da mummunan tasirin sauyin yanayi.

 

“Ta hanyar haɗin gwiwa da himma tare, za mu iya gina Nijeriya mai ɗorewa da juriya.

 

“A wannan rana ta Ranar Rediyo ta Duniya, mu yi alƙawarin kawo sauyi da kare duniyar mu domin amfanin zuriyar da ke tafe.”

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a kan sauyin yanayi

এছাড়াও পড়ুন:

FG Ta Jaddada Bukatar Samarda Sabbin Ka’idojin Visa Domin Taimakawa Kasuwancin A Duniya

 

Gwamnatin Tarayya tayi kira don samun tsarin visa mai sassauci ga kamfanonin Najeriya da ke neman kafa masana’antu da kasuwanci a ƙasashen waje.

 

Ministan Yada Labarai da Wayarda Kan Jama’a, Mohammed Idris, shine ya yi wannan kiran a Addis Ababa, Ethiopia, yayin da ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a wani taro da mambobin gudanarwa na Al’ummar Najeriya a Ethiopia, a cikin tattaunawa da aka yi a wajen zama na 38 na Taron Shugabannin Kasashe na Tarayyar Afirka (AU).

 

Ya jaddada cewa, yayin da Najeriya ke ci gaba da samar da yanayi mai kyau ga kamfanonin waje don zuba jari da aiki cikin ƙasar, yana da kyau da kuma amfanar juna ga sauran ƙasashen duniya su ba da irin wannan tallafi ga kasuwancin Najeriya da ke son faɗaɗa a duniya.

 

“A cikin shekarar da ta gabata, na wakilci Najeriya a Indonesia kuma na gano cewa akwai kamfanoni 50 na manyan kamfanoni na Indonesia suna aiki a Najeriya amma ba mu da kamfanoni guda biyar na Najeriya da suke aiki a Indonesia. Idan suna son zuwa ƙasarmu don kasuwanci saboda yawan jama’armu da ikon siyan kayayyaki da ayyukansu, to ya kamata a samu tsarin cudeni in cudeka da za a ba da dama ga ‘yan Najeriya; kuma matsalar visa ita ce wannan matsalar da ake samu a Ethiopia da Indonesia. Yana da wahala sosai ga mutane su ba ‘yan Najeriya visa,” in ji shi.

 

Da yake magana akan batun soke visa na e-visa da Visa-on-Arrival na gwamnati ta Ethiopia ga matafiya daga Najeriya, Idris ya tabbatar da cewa wannan zai mika shine ga Ministan Harkokin Waje don samun cikakken tattaunawa ta diflomasiyya.

 

Ya kuma nuna damuwarshi da halin da ‘yan Najeriya a Ethiopia suke fuskanta, Ministan ya jaddada cewa manufofin visa tsakanin ƙasashe yawanci suna bisa ka’idar amana ce.

 

Ya bayyana cewa gwamnatoci suna aiwatar da ƙa’idojin visa a matsayin martani ga manufofin da aka ba wa ‘yan ƙasashensu, yana mai nuna muhimmancin samun yarjejeniyoyi masu daidaito da amfanar juna a cikin tafiyar da harkokin kasashen waje da diflomasiyya.

 

“Duk wata dangantaka da sauran ƙasashe tana bisa ka’idar amana. Don haka, idan mun ba su Visa-on-Arrival, babu dalilin da zai sa su kasa baza su ba mu Visa-on-Arrival ba” in ji shi.

 

Ministan ya yi kira ga ‘yan Najeriya da ke zaune a ƙasashen waje su ci gaba da nuna kyakkyawan hali da zama ɗan kasa mai alhakin don inganta matsayin ƙasarsu Nigeria a idon duniya.

 

Ministan ya yi amfani da wannan dama don sanar da al’ummar Najeriya game da manufofin gwamnatin Tinubu, yana jaddada cewa an samu nasarori masu yawa wajen farfado da tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa, dakile rashin tsaro, da dawo da martabarta ga masu zuba jari a Najeriya.

 

Idris ya ce Najeriya ta samu kimanin dala miliyan 1.07 a cikin zuba jari na waje (FDI) domin kafa masana’antu na magunguna da kayan magani.

 

Ya jaddada cewa wannan zuba jari mai muhimmanci yana nuni da farawa na masana’antar magungunan Najeriya ta hanyar sanya ƙasar a matsayin babban mai ruwa da tsaki a samar da magunguna, kara ƙarfin samar da magunguna na cikin gida, rage dogaro da kayayyaki daga waje, ƙirƙirar ayyukan yi, da ƙarfafa sashen lafiya na ƙasar.

 

Ministan ya bayyana cewa a cikin kwanaki ƙasa da 250, an rarraba Naira biliyan 32 ga ɗalibai a ƙarƙashin Tsarin Lamunin Ɗalibai don tabbatar da cewa babu ɗalibi da zai rasa damar samun ilimi mai kyau saboda rashin kuɗi.

 

Idris, wanda ya tabbatar da alkawarin gwamnati wajen magance matsalolin tsaro, ya bayyana cewa a cikin shekarar 2024 kawai, hukumomin tsaro sun kashe ‘yan ta’adda da masu laifi 8,000, sun ceto mutane 8,000 da aka sace, kuma sun samu kama mutane 11,600.

 

Ministan ya bayyana cewa hanyar Kaduna-Abuja, wacce a da take da matsalolin laifi, yanzu an tsaftace ta daga abubuwan laifi, yana mai cewa ingantaccen tsaro a wannan hanya ya kawo babban sauƙi ga masu tafiya.

 

Idris ya ce gyara wani abu ne mai wahala sosai amma akwai ci gaba mai kyau zuwa wadata ga kowa kamar yadda shugaban kasa ya yi alkawari.

 

A cikin jawabin sa, Shugaban Al’ummar Najeriya a Ethiopia, Mr. Muideen Alimi, ya ce wani ɓangare na shirin aikinsu shi ne haɗin gwiwa da Hukumar ‘Yan Najeriya a Diaspora don shirya taron ƙwararru kan ƙarfafa ci gaban tattalin arziki ta hanyar cinikayya a cikin Afirka.

 

Ya roki Najeriya ta tallafa wajen cimma wannan shirin na kafa Babban Bankin Afirka da kuma samun ƙarfi a Cibiyar Kuɗaɗen Afirka.

 

Taron ya samu halartar Darakta Janar na Hukumar ‘Yan Najeriya a Diaspora, Mrs. Abike Dabiri-Erewa, da sauran manyan jami’an gwamnati.

 

Rel/Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin Sin Masu Zaman Kansu Na Taka Rawar Gani Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Majalisa ta tsayar da ranar sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin Dokar Haraji
  • Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba
  • Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata
  • Kasar Iran Zata Aika Da Tawaga Mai Karfi Zuwa Jana’izar Sayyid Nasarallah
  • FG Ta Jaddada Bukatar Samarda Sabbin Ka’idojin Visa Domin Taimakawa Kasuwancin A Duniya
  • Gwamnati Ta Buƙaci Sauƙaƙa Tsarin Samar Da Biza Don ƙarfafa Kasuwancin ‘Yan Nijeriya A Duniya
  • Nijar Na Son Kulla Yarjejeniya Kafofin Yada Labarai Na Iran
  • Hukumar Kula Da Ayyukan Duba-gari Ta Kasa Za Ta Karrama Shugaba Tinubu