Aminiya:
2025-02-20@08:48:38 GMT

Kotu ta yanke hukuncin sare hannun matashi kan sare hannun yaro a Gombe

Published: 13th, February 2025 GMT

Babbar Kotun Jiha ta 5 a Gombe, ƙarƙashin Jagorancin Mai Shari’a A.M. Haruna, ta yanke wa wani matashi mai suna Abdullahi Suleiman hukuncin sare masa hannu, bisa samunsa da laifin sare hannun wani yaro mai suna Khalifa Abubakar, ɗan shekara 14 da adda.

Lamarin ya faru ne a ranar 12 ga watan Fabrairu, shekarar 2022, a garin Moddibo da ke Ƙaramar hukumar Yamaltu Deba, a jihar ta Gombe lokacin wani bikin aure da ya rikiɗe ya koma rikici da misalin ƙarfe 11 na dare yayin da angon ya kori duk wanda ke wajen saboda hayaniyar da ta kaure.

Ba zan daina sukar gwamnatin Tinubu ba — Farfesa Yusuf Sojoji sun doki ’yan sanda kan kama ‘mai laifi’

A lokacin fitar jama’a daga wajen bikin, Abdullahi Suleiman, wanda ya fito daga ƙauyen Wajari, ya yi amfani da adda wajen tarwatsa jama’a tare da wasu matasa.

Khalifa Abubakar, wanda takalminsa ya faɗi a wajen gudu, ya tsaya don ɗauka, amma Abdullahi ya kai masa sara da adda har ya sare masa hannun dama gaba ɗaya.

’Yan uwan Khalifa sun gaggauta kai shi Asibitin Koyarwa na Gwamnatin Tarayya da ke Gombe, inda aka masa jinya bayan sare masa hannun.

Bayan faruwar lamarin, ‘yan uwan Khalifa sun kai ƙara ofishin ‘yan sanda da ke Deba. Sai dai daga baya an ba da belin Abdullahi Suleiman. Wannan ya sa gwamnati ta shiga lamarin, inda lauyan gwamnati, Barista Y.G. Ahmad, ya shigar da ƙara a gaban Babbar Kotun Jiha ta 5. Karar mai lamba GM/88c / 2022

A yayin shari’ar, kotun ta saurari shaidu biyar daga ɓangaren mai ƙara, ciki har da Khalifa Abubakar, waɗanda suka tabbatar cewa Abdullahi Suleiman ne ya aikata laifin.

Daga cikin shaida uku, sun kasance shaidun gani da ido da suka tabbatar da cewa Abdullahi ne ya sari Khalifa a lokacin rikicin.

Likitan da ya duba Khalifa shi ma Kotu ta gayyato shi ya bada shaidar jinyar da ya yi masa.

A ɓangaren wanda ake kara kuwa shaidu biyu ya gabatar wa kotu amma ba su bayar da hujjoji masu ƙarfi ba. inda bayan tantance shaidun, kotu ta tabbatar da laifin da ake tuhumar Abdullahi Suleiman akai.

Bayan tabbatar da laifin, kotu ta yi la’akari da yadda Abdullahi Suleiman ya nemi afuwa tare da nuna nadama. Sai dai Lauyan sa, Y.A. Waziri, ya roƙi kotu ta amince su saya wa Khalifa hannun roba, amma kotu ta ƙi yarda da wannan roƙo.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Koto sare hannun matashi Yamaltu Deba

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne

A ranar 15 ga watan Fabrairu, ministocin harkokin waje na kasashen Amurka, Japan, da Koriya ta Kudu sun yi shawarwari a Munich na kasar Jamus. A cikin sanarwar hadin gwiwar da suka fitar, a karon farko, sun bayyana goyon bayansu ga yadda Taiwan za ta shiga cikin kungiyoyin kasa da kasa da suka dace, tare da jaddada muhimmancin wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan. Dangane da wannan batu, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Guo Jiakun, ya sake nanata cewa, Taiwan wani bangare ne na kasar Sin da ba za a iya raba shi da ita ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gidan kasar Sin kawai, kuma ba ta yarda da wata tsangwama daga waje ba. Shigar Taiwan cikin ayyukan kungiyoyin kasa da kasa dole ya kasance bisa ka’idar Sin daya tak a duniya. A ko da yaushe kasar Sin tana adawa da yadda wasu kasashe ke hada kai wajen kafa kananan kungiyoyi, da tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasar Sin, tare da suka da bata wa kasar Sin suna, da tayar da husuma da adawa, kana ta mika wa kasashen da abin ya shafa gamsasshen korafi.

Bugu da kari, a matsayin martani ga kwaskwarimar da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta yi kan takardar sahihancin bayanai kan dangantakar Amurka da Taiwan, Guo Jia Kun ya bukaci bangaren Amurka da ya gaggauta gyara kuskuren, da kuma mutunta ka’idar Sin daya tak da sanarwoyi guda uku na Sin da Amurka, kuma ta bi a hankali wajen tinkarar batun Taiwan. (Mohammed Yahaya)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • Gwamnatin Gombe ta horar da makiyaya kan sabbin hanyoyin kiwo
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Irin Gagarumar Rawar Da Iran Ta Taka A Fegen Tsaro Yakin Tekun Pasha
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • Kotu ta hana Gwamnatin Tarayya riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano
  • Kotu Ta Dakatar Da Gwamnatin Tarayya Daga Riƙe Wa Ƙananun Hukumomin Kano 44 Kuɗaɗensu
  • Kotu Ta Hana Gwamnatin Tarayya Riƙe Wa Kano Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomi
  • Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi