HausaTv:
2025-04-13@09:52:24 GMT

Iran A Shirye Take Ta Kare Kanta Cikin Karfi Daga Duk Wani Hari Da Za A Kawo Ma Ta

Published: 13th, February 2025 GMT

Kwamandan sojan na Iran  Birgediya Janar Hamid Wahidi ya bayyana cewa, Iran tana da cikakken shirin na aiwatar da umaranin babban kwamandan sojin kasa, kuma akidarmu ta yaki, ta ginu ne akan kariya, amma kuma a lokaci daya za mu fuskanci duk wanda ya kawo mana hari, da karfi.

Birgediya  janar Hamid Wahidi ya bayyana hakan ne dai a lokacin bikin kaddamar da lambobin yabo da sadaukarwa ga iyalan shahidai na sojan sama, inda ya ce: “A wannan lokacin da ake ciki, Muna cikin wani yanayi mai matukar hatsari a duniya, amma a ranar sojan sama jagoran juyin juya halin musulunci ya shata mana ka’idoji masu kima da za mu yi aiki da su da, kuma za su kasance wadanda za mu yi aiki da su a kodayaushe.

Kwamandan sojan saman na Iran ya kara da cewa; A halin da ake ciki a yanzu sojan saman Iran suna da karfi sosai, sun kuma dogara ne da kansu wajen kera abubuwan da suke da bukatuwa da su.

Har ila yau Birgediya Janar Hamid Wahidi ya ce, yana alfahari da dukkanin abokan aikinsa sojojin sama masu jarunta wadanda su ka tabbatar da hakan a lokacin farmakin “Wa’adus-sadiq”. Haka nan kuma  ba za su taba ja da baya ba a karkashin kowane yanayi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji

Kamfanin Media Trust Limited na farin cikin sanar da al’umma cewa daga ranar Juma’a 11 ga watan Afrilun 2025, Rediyonta na Tusts Radio zai fara shirye-shiryen gwaji.

Tashar za ta fara yaɗa shirye-shiryenta a kan mita 92.7 a zangon FM a birnin tarayya Abuja da kewaye, kuma wannan na daga cikin tsare-tsaren da kamfanin ke bi na faɗaɗa aikin watsa labarai sama da shekaru 27 a Nijeriya.

An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta

Kamfanin Media Trust shi ne mai wallafa jaridun Daily Trust da Aminiya a Nijeriya kuma mamallakin Trust TV da kuma Trust Radio a yanzu.

Ga waxanda ba su a birnin tarayya Abuja ko kuma suka yi tafiya za su iya kama tashar a shafinta na intanet a https://trustradio.com.ng ko a manhajar Radio Garden.

Haka kuma za a iya saurarenta shafukan Aminiya da Daily Trust da shafukan sada zumunta.

Da zarar tashar ta kammala gwajin za ta fara watsa ƙayatattun shirye-shirye da labarai tare da rahotanni masu ilimantarwa, faxakarwa tare da nishaɗantarwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi
  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 17: Tinubu Ya Kare Yadda Gwamnatinsa Ke Tafiyar Da Tsarin Rabon Arzikin Kasa
  • Waraka Daga Bashin Ketare
  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Sojojin Sama Na HKI Kimani 1000 Guda New Suka Bukaci A Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji
  • Pezeshkian : Jagora bai shi da adawa da Amurkawa masu zuba jari a Iran