Malaman Firamare sun sake tsunduma yajin aiki kan rashin albashi a Abuja
Published: 13th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Ƙasa (NUT) da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Ƙasa (NULGE), sun umarci malaman makarantun firamare da ke ƙarƙashin Sashen Ilimin Ƙananan Hukumomi (LEA) da su sake tsunduma yajin aiki.
Haka kuma an umarci ma’aikatan ƙananan hukumomi shida na Babban Birnin Tarayya, da su dakatar da aiki daga ranar Alhamis, 13 ga watan Fabrairu, 2025, sakamakon rashin biyan mafi ƙarancin albashin Naira 70,000 da shugabannin ƙananan hukumomi suka yi.
Shugaban Ƙungiyar NUT reshen Abuja, Kwamared Mohammed Shafas, ya bayyana cewa ƙungiyoyin sun yanke shawarar sake komawa yajin aikin ne saboda gazawar shugabannin ƙananan hukumomi shida wajen aiwatar da mafi ƙarancin albashi.
Ya tunatar da cewa malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi sun dakatar da yajin aiki a ranar 12 ga watan Disamban 2024 ne, bayan da aka sanya hannu kan yarjejeniya tsakanin ƙungiyoyin ƙwadago da shugabannin ƙananan hukumomi.
Ya ce an yi yarjejeniyar ne domin fara aiwatar da biyan albashin Naira 70,000 daga watan Janairun 2025.
Sai dai, duk da hakan, shugabannin ƙananan hukumomin sun yi watsi da yarjejeniyar.
Kwamared Shafas, ya ƙara da cewa ba wai rashin aiwatar da mafi ƙarancin albashin ne kaɗai ya jawo yajin aikin ba, har da gazawar shugabannin wajen biyan wasu haƙƙoƙin ma’aikata.
Ya ce buƙatun da ba a biya ba sun haɗa da kashi 40 na alawus-alawus, ƙarin albashi na kashi 25 da 35.
Ya ce, sai an biya waɗannan haƙƙoƙi kafin malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi su koma bakin aiki a Abuja.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ma aikatan Ƙananan Hukumomi malaman firamare
এছাড়াও পড়ুন:
Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a Tehran ya bayyana cewa; Tun cin nasarar juyin musulunci, Iran ta zabi hanyar tattaunawa, saboda ta tabbatar da kyakkyawar niyyarta da kuma aiki da hankali a mu’amalrta da duniya.
Limamin na Tehran Ayatullah Saiddiki ya ce, a yayin tattaunawar da za a yi a tsakanin Iran da Amurka wacce za ta kasance ta hanyar shiga tsakani, Iran za ta ji abinda daya bangaren zai fada, sannan kuma ta bayar da jawabi, domin tabbatarwa da duniya cewa ita daula ce mai aiki da hankali, kuma ba ta tsoron tattaunawa.
Ayatullah Siddiki ya yi ishara da zancen jagoran juyin musulunci akan yadda bangaren da ake tattaunawar ba ya aiki da abubuwan da aka cimmawa da amincewa da su.
Haka nan kuma limamin na Tehran ya ambato jagoran juyin musuluncin na Iran yana bayyana yadda Amurka take kiyayya da Jamhuriyar da musulunci na Iran da addinin musulunci da kuma alkur’ani mai girma, saboda asarar manufofinta da ta yi a cikin Iran.
Ayatullah Siddiki ya kuma amabci cewa maganar da shugaban kasar Amurka yake yi na tattaunawa kai tsaye da Iran ba koma ba ne, sai yaudara da ba ta da tushe. Kuma saboda yadda Amurka ba ta aiki da duk wata yarjejeniya da aka cimmawa, don haka zama da ita gaba da gaba domin tattaunawa bai dace da mu ba.
Har ila yau, ya kuma ce, Shirin Iran na Nukiliya na zaman lafiya yana ci gaba da samun bunkasa saboda jagoranci na hikima na jagoran juyin juya halin musulunci.