Aminiya:
2025-03-22@13:50:36 GMT

Malaman Firamare sun sake tsunduma yajin aiki kan rashin albashi a Abuja

Published: 13th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Ƙasa (NUT) da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Ƙasa (NULGE), sun umarci malaman makarantun firamare da ke ƙarƙashin Sashen Ilimin Ƙananan Hukumomi (LEA) da su sake tsunduma yajin aiki.

Haka kuma an umarci ma’aikatan ƙananan hukumomi shida na Babban Birnin Tarayya, da su dakatar da aiki daga ranar Alhamis, 13 ga watan Fabrairu, 2025, sakamakon rashin biyan mafi ƙarancin albashin Naira 70,000 da shugabannin ƙananan hukumomi suka yi.

An yanke hukuncin sare hannun matashi kan sare hannun yaro a Gombe Ba zan daina sukar gwamnatin Tinubu ba — Farfesa Yusuf

Shugaban Ƙungiyar NUT reshen Abuja, Kwamared Mohammed Shafas, ya bayyana cewa ƙungiyoyin sun yanke shawarar sake komawa yajin aikin ne saboda gazawar shugabannin ƙananan hukumomi shida wajen aiwatar da mafi ƙarancin albashi.

Ya tunatar da cewa malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi sun dakatar da yajin aiki a ranar 12 ga watan Disamban 2024 ne, bayan da aka sanya hannu kan yarjejeniya tsakanin ƙungiyoyin ƙwadago da shugabannin ƙananan hukumomi.

Ya ce an yi yarjejeniyar ne domin fara aiwatar da biyan albashin Naira 70,000 daga watan Janairun 2025.

Sai dai, duk da hakan, shugabannin ƙananan hukumomin sun yi watsi da yarjejeniyar.

Kwamared Shafas, ya ƙara da cewa ba wai rashin aiwatar da mafi ƙarancin albashin ne kaɗai ya jawo yajin aikin ba, har da gazawar shugabannin wajen biyan wasu haƙƙoƙin ma’aikata.

Ya ce buƙatun da ba a biya ba sun haɗa da kashi 40 na alawus-alawus, ƙarin albashi na kashi 25 da 35.

Ya ce, sai an biya waɗannan haƙƙoƙi kafin malaman firamare da ma’aikatan ƙananan hukumomi su koma bakin aiki a Abuja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ma aikatan Ƙananan Hukumomi malaman firamare

এছাড়াও পড়ুন:

Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki

Iran ta yi Allah wadai da Kwamitin Sulhun na MDD na rashin tabaka komai wajen  dakatar da ayyukan Amurka da Isra’ila wanda Iran din ta bayyana da abin kunya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya yi tir da munanan hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Yemen da kuma yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kai wa Falasdinawa hari a zirin Gaza, tare da yin Allah wadai da rashin daukar wami mataki daga kwamitin sulhu na fuskantar wadannan munanan ayyukan.

Esmaeil Baghaei, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana matukar na dama kan yadda ake kashe fararen hula da suka hada da mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata muhimman ababen more rayuwa na kasar Yemen, sakamakon hare-haren da Amurka ke kaiwa.

Ya bayyana hare-haren da Amurka ta kai ta sama a matsayin laifukan yaki da laifukan ta’addanci, yana mai danganta hakan da “abin kunya da rashin gaskiya” na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da sauran cibiyoyin kasa da kasa kan wannan ta’asa.

Ya ce Amurka da gwamnatin yahudawan sahyoniya sun kitsa wani shiri na hadin gwiwa na raunana al’ummar musulmi da kuma rufe duk wata muryar goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta.

Daga karshe Baghaei ya jaddada nauyin da ya rataya a wuyan kasashen musulmi na duniya na dakatar da zaluncin da Isra’ila ke yi da kuma hare-haren da sojojin Amurka suke yi a kan Falasdinawa da sauran al’ummar musulmi, yana mai kira ga gwamnatocin musulmi da su dauki matakin da ya dace da kuma kokarin da kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ke yi na shawo kan lamarin.

Akalla Falasdinawa 436 da suka hada da kananan yara 183 ne aka kashe tun bayan da Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza a ranar Talata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Wike Ya Kwace Filaye 4,794 A Abuja Saboda Rashin Biyan Kudin Ka’ida
  • Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa
  • Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci
  • Gwamna Yusuf Ya Yi Sabbin Nade-Nade A Kano
  • Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki
  • Mun Yi Watsi Da Ayyana Dokar Ta-Ɓaci Da Tinubu Ya Yi A Ribas – Shugabannin Adawa
  • Dakarun Qassam sun harba makami mai linzami a kan Tel Aviv
  • Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi
  • Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja