Aminiya:
2025-02-20@09:10:50 GMT

Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas

Published: 13th, February 2025 GMT

Hukumar hana fasa kwauri ta Najeriya (Kwastam) reshen yanki 2 da ke Onne a Jihar Ribas tare da haɗin gwiwar ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro sun lalata kimanin kwantena 60 na kayayyakin da ba su da inganci da magungunan da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba.

Kayayyakin da  kuɗinsu ya haura Naira biliyan 100.

Lamarin ya faru ne a wurin da ake zubar da shara a Jihar Ribas daura da titin filin jirgin sama na Fatakwal a ranar Laraba.

Malaman Firamare sun sake tsunduma yajin aiki kan rashin albashi a Abuja Ba zan daina sukar gwamnatin Tinubu ba — Farfesa Yusuf

Da yake jawabi a wurin da aka gudanar da aikin, mataimakin shugaban hukumar hana fasa kwauri ta Kwastam daga sashin tabbatar da doka da bincike na Kwastam, Timi Bomodi, ya ce wannan aiki na haɗin gwiwa ne da kwamitin da aka kafa wanda mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ya kafa.

Bomodi, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin da ke kula da lalata magunguna da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba, ya ce, “Kwamiti ne da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro ya kafa wanda ya ƙunshi dukkan hukumomin da suka dace.

“Saboda haka, muna nan a yau don aiwatar da babban maƙasudin aikin, wanda shi ne lalata irin wannan. Aikin da aka bai wa wannan kwamiti shi ne gano da ware kayayyakin da lalata magungunan da aka shigo da su ƙasar nan ba bisa ƙa’ida ba.

“A nan Fatakwal, muna lalata kimanin kwantena 64 masu tsawon ƙafa 40 da darajar kuɗinsu ta kai ɗaruruwan biliyoyin Naira.

“Kuma kamar yadda yake a yau, muna aiwatar da aikin ba tare da tsoro ko yi wa wasu alfarma ba, kuma muna aika saƙo a bayyane ga duk masu irin wannan aiki da ya kamata su daina.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwastam

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5

Gwamnatin tarayya ta ce ta bai wa gwamnatin jihar Jigawa tallafin kayayyakin noma na sama da naira biliyan 5 domin bunkasa noman abinci a fadin jihar.

 

 

Ministan noma da samar da abinci Sanata Abubakar Kyari ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a garin Dabi da ke karamar hukumar Ringim a bikin ranar manoman alkama ta bana.

 

Ya bayyana cewa, matakin na daga cikin kudirin gwamnatin tarayya na tallafawa jihar wajen bunkasa noma domin kasuwanci.

 

Sanata Kyari ya yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya ta gamsu sosai da yadda gwamnatin jihar Jigawa da manoma suka yi, na rungumar ayyukan noman rani.

Ministan ya yaba da kokarin gwamnatin jihar Jigawa da manoma, bisa goyon bayan shirin gwamnatin tarayya na bunkasa noman alkama,  ta hanyar samar da kayan amfanin gona da dabarun zamani.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na bullo da wasu tsare-tsare da za su samar da guraben ayyukan yi da wadata kasa da abinci.

A cewarsa, tuni ya sayo taraktoci 300, ingantattun irin shuka, da sauran kayayyakin aikin gona domin noman amfanin gona daban-daban a fadin kananan hukumomin jihar 27.

Tun da farko a jawabinsa na maraba kwamishinan noma da albarkatun kasa na jihar Alhaji Muttaqa Namadi ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta bayar da tan 3,500 na ingantaccen irin alkama, da injinan ban ruwa 10,000 domin tallafawa noman alkama a jihar.

Ministan da mukarrabansa da Gwamna Umar Namadi sun ziyarci gonakin alkama da dama a Yakasawa da Dabi a karamar hukumar Ringim.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, kayayyakin da gwamnatin tarayya ta bayar sun hada da injinan ban ruwa 10,000, da lita 10,000 ta maganin kwari, taki na ruwa da injinan feshi.

Wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, Darakta Janar na Gidan Rediyon Tarayya FRCN, Dr Mohammed Bulama,  da sarakuna da malaman addini, da wakilan kungiyar sarrafa fulawa ta kasa, da manoman alkama da wasu manyan jami’an gwamnati.

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Haramta Amfani Da Tankoki Masu Ɗaukar Lita 60,000 Aiki Daga Maris 1
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama
  • An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara
  • Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5
  • Tara Daga N100,000 Kan Amfani Da Mitar Wutar Lantarki Ta Ɓarauniyar Hanya – NERC
  • Hamas Ta Sanar Da Shahadar Wani Jagoranta Da HKI Ta Kashe A Lebanon
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Tituna Akan Kudi Naira Biliyan 6.3