Tirela ta murƙushe ɗaliba har lahira a Bauchi
Published: 13th, February 2025 GMT
Wata ɗalibar a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya da ke Bauchi, Faith Aluko Adesola, ta rasa ranta bayan da wata babbar mota ta murƙushe ta.
Jami’in hulɗa da jama’a na makarantar, Alhaji Rabi’u Muhammad ne, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Majalisun Tarayya sun amince da kasafin kuɗin N54.9trn na 2025 Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a RibasYa ce Adesola ɗaliba ce da ke ajin farko (ND1) a Sashen Koyon Aikin Jarida na makarantar.
A cewarsa, tana kan ɗan acaba domin zuwa makaranta lokacin da babbar motar ta yi awon gaba da babur ɗin a kusa da kofar shiga makarantar, lamarin da ya yi sanadiyyar rasuwarta.
“Da muka samu labarin, tawagar makaranta da suka haɗa da shugaban tsaro da shugaban kula da harkokin ɗalibai sun garzaya wajen, amma likitan makaranta ya tabbatar da rasuwarta,” in ji Muhammad.
Direban babur ɗin ya tsira da ransa a hatsarin.
Makarantar ta sanar da iyayenta, kuma wakilanta sun halarci jana’izarta a ranar Alhamis.
Muhammad, ya ja hankalin ɗalibai da su kasance masu taka-tsantsan yayin ƙetare hanya domin gujewa irin wannan hatsari.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai hatsarin mota kwaleji rasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Hisbah Ta Lalata Katan 51 Na Giya a Jihar Yobe
Ya ce shan giya yana barazana ga lafiyar jama’a tare da haddasa matsalolin zamantakewa.
A cewarsa, hana yaɗuwar giya zai rage aikata laifuka da kuma inganta zaman lafiya.
Dr. Yahuza ya kuma buƙaci al’umma da su mara wa Hisbah baya ta hanyar bayar da rahoto kan duk wani abu da ke saɓa wa doka.
Ya tabbatar da cewa hukumar ta ƙudiri aniyar ci gaba da aiki don tabbatar da adalci, zaman lafiya da gyara halayyar al’umma a Jihar Yobe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp