Aminiya:
2025-02-20@08:56:01 GMT

An kama likita kan laifin yi wa ’yan bindiga magani a Katsina

Published: 13th, February 2025 GMT

Jami’an tsaro sun kama wani ma’aikacin lafiya da ake zargi da yi wa wasu ’yan bindiga da suka raunata magani a Ƙaramar hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Daga cikin majinyatan nasa har da ƙasurmin da ake nema Usman Modi Modi, wanda aka sanar da bada ladar Naira miliyan 50 don nemo shi.

Tirela ta murƙushe ɗaliba har lahira a Bauchi Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas

A cikin wani bidiyo da wani mai sharhi kan harkokin tsaro Zagazola Makama ya samu, wanda ake zargin mai suna Lawan Ado, ya amsa laifin jinyar wasu ’yan bindiga da suka jikkata.

A cikin bidiyon, ya ce ’yan bindigar za su ɗauke shi su kai shi maɓoyarsu a duk lokacin da suke buƙatar magani don neman lafiya.

A cewarsa, ɗan bindigan da ya fara yi wa magani shi ne Usman Modi Modi bayan da shugaban ƙungiyar su ya samu raunuka a wata arangama da ƙungiyar ’yan banga ta Yan Kyanbara.

“Da farko an kai shi wani asibiti a Taskiya domin yi masa magani, amma bayan kwana biyu, sai suka kawo ni don in ƙara yi masa magani. An biya ni Naira 18,000 don kula da lafiyar waɗanda aka raunata,” cewar likitan da ake zargin.

Ado ya ƙara da cewa yana jinyar wasu manyan ’yan bindiga da suka haɗa da Mai Kudi wanda ya biya shi Naira 8,000 bayan an harbe shi a Kurfi.

Ya ce, haka ma ya yi wa Audu, mai taimaka wa Usman Modi Modi, wanda shi ma ya biya Naira 8,000.

Ya ƙara da cewa, “Dogo Mardi, wanda ya samu raunin harbin bindiga a yayin wani harin fashi da makami ya biya ni N11,000”.

Ya bayyana cewa ya yi tafiya zuwa wasu wurare domin jinyar ’yan fashi, ciki har da wanda aka bayyana da Karanboguwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar Safana yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane

A yunƙurin daƙile ta’adar garkuwa da mutane, Majalisar Dokokin Jihar Edo, ta amince da dokar zartar da hukuncin kisa kan duk wanda aka kama da laifin.

Majalisar ta amince da ƙudirin ne wanda ta yi wa bita daki-daki yayin zaman da ta gudanar a ranar Talata.

USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Charity Aiguobarueghian ne ya jagoranci gabatar da ƙudirin wanda shugaban marasa rinjaye, Henry Okaka ya goyi baya.

A baya dai Majalisar Dokokin Edo ta ayyana hukuncin ɗaurin rai da rai ga duk wanda aka tabbatar wa laifin garkuwa da mutane tare da ƙwace duk wani abu da mallaka a dalilin aikata ta’adar ta garkuwa da neman kuɗin fansa.

Sai dai a yanzu majalisar dokoki ta sahale a tsananta matakin da za a riƙa ɗauka zuwa hukuncin kisa haɗi da ƙwace duk abin da aka mallaka ta hanyar aikata laifin.

Tuni dai Kakakin Majalisar, Blessing Agbebaku ya umarci Magatakardan majalisar da ya miƙa wa Gwamna Godwin Obasake ƙudirin domin amincewa.

Kazalika, majalisar ta amince da ƙudirin yi wa dokokin hukumomin samar da wutar lantarkin jihar gyaran fuska.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri
  • Hamas Ta Sanar Da Shahadar Wani Jagoranta Da HKI Ta Kashe A Lebanon
  • Da Dama Sun Rasu Yayin Da NAF Ta Kai Wa ‘Yan Bindiga Hari A Katsina
  • Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon
  • Gwamnati ta raba wa mata tallafin awakai na N5bn a Katsina
  • Gwamnati ta kashe N5bn domin bai wa mata tallafin kiwon awakai a Katsina