Aminiya:
2025-04-14@18:05:38 GMT

An kama likita kan laifin yi wa ’yan bindiga magani a Katsina

Published: 13th, February 2025 GMT

Jami’an tsaro sun kama wani ma’aikacin lafiya da ake zargi da yi wa wasu ’yan bindiga da suka raunata magani a Ƙaramar hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Daga cikin majinyatan nasa har da ƙasurmin da ake nema Usman Modi Modi, wanda aka sanar da bada ladar Naira miliyan 50 don nemo shi.

Tirela ta murƙushe ɗaliba har lahira a Bauchi Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas

A cikin wani bidiyo da wani mai sharhi kan harkokin tsaro Zagazola Makama ya samu, wanda ake zargin mai suna Lawan Ado, ya amsa laifin jinyar wasu ’yan bindiga da suka jikkata.

A cikin bidiyon, ya ce ’yan bindigar za su ɗauke shi su kai shi maɓoyarsu a duk lokacin da suke buƙatar magani don neman lafiya.

A cewarsa, ɗan bindigan da ya fara yi wa magani shi ne Usman Modi Modi bayan da shugaban ƙungiyar su ya samu raunuka a wata arangama da ƙungiyar ’yan banga ta Yan Kyanbara.

“Da farko an kai shi wani asibiti a Taskiya domin yi masa magani, amma bayan kwana biyu, sai suka kawo ni don in ƙara yi masa magani. An biya ni Naira 18,000 don kula da lafiyar waɗanda aka raunata,” cewar likitan da ake zargin.

Ado ya ƙara da cewa yana jinyar wasu manyan ’yan bindiga da suka haɗa da Mai Kudi wanda ya biya shi Naira 8,000 bayan an harbe shi a Kurfi.

Ya ce, haka ma ya yi wa Audu, mai taimaka wa Usman Modi Modi, wanda shi ma ya biya Naira 8,000.

Ya ƙara da cewa, “Dogo Mardi, wanda ya samu raunin harbin bindiga a yayin wani harin fashi da makami ya biya ni N11,000”.

Ya bayyana cewa ya yi tafiya zuwa wasu wurare domin jinyar ’yan fashi, ciki har da wanda aka bayyana da Karanboguwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar Safana yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina

A wannan Litinin ɗin ce ne aka rantsar da sabbin shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Jihar Katsina waɗanda aka gudanar da zaɓensu a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025.

Babban Jojin Jihar Katsina, Mai Shari’a Musa Danladi Abubakar ne ya jagoranci rantsar da sabbin shugabannin ƙananan hukumomin.

’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato

Sai dai gab da lokacin da za a rantsar da su, ɗaya daga cikinsu ya faɗi ya sume a lokacin da yake ƙoƙarin shiga rumfar da aka tanadar masu.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Bakori Honarabil Aminu Ɗan Hamidu shi ne wanda ya faɗi kuma aka ɗauka ranga-ranga zuwa asibiti.

Binciken da muka yi ya nuna cewa, shugaban ya take wani sashe na babbar rigar shi ne ba tare da ya yi la’akari ba yayin da ya yunƙura da ƙarfi don hawa matattakalar shiga rumfar, lamarin da ya janyo rigar ta shaƙe shi ya faɗi a sume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • Firaministan Kasar Laos: Kasar Sin Abar Koyi Ce a Fannin Kawar Da Talauci
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13