Aminiya:
2025-03-25@14:04:55 GMT

An kama likita kan laifin yi wa ’yan bindiga magani a Katsina

Published: 13th, February 2025 GMT

Jami’an tsaro sun kama wani ma’aikacin lafiya da ake zargi da yi wa wasu ’yan bindiga da suka raunata magani a Ƙaramar hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Daga cikin majinyatan nasa har da ƙasurmin da ake nema Usman Modi Modi, wanda aka sanar da bada ladar Naira miliyan 50 don nemo shi.

Tirela ta murƙushe ɗaliba har lahira a Bauchi Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas

A cikin wani bidiyo da wani mai sharhi kan harkokin tsaro Zagazola Makama ya samu, wanda ake zargin mai suna Lawan Ado, ya amsa laifin jinyar wasu ’yan bindiga da suka jikkata.

A cikin bidiyon, ya ce ’yan bindigar za su ɗauke shi su kai shi maɓoyarsu a duk lokacin da suke buƙatar magani don neman lafiya.

A cewarsa, ɗan bindigan da ya fara yi wa magani shi ne Usman Modi Modi bayan da shugaban ƙungiyar su ya samu raunuka a wata arangama da ƙungiyar ’yan banga ta Yan Kyanbara.

“Da farko an kai shi wani asibiti a Taskiya domin yi masa magani, amma bayan kwana biyu, sai suka kawo ni don in ƙara yi masa magani. An biya ni Naira 18,000 don kula da lafiyar waɗanda aka raunata,” cewar likitan da ake zargin.

Ado ya ƙara da cewa yana jinyar wasu manyan ’yan bindiga da suka haɗa da Mai Kudi wanda ya biya shi Naira 8,000 bayan an harbe shi a Kurfi.

Ya ce, haka ma ya yi wa Audu, mai taimaka wa Usman Modi Modi, wanda shi ma ya biya Naira 8,000.

Ya ƙara da cewa, “Dogo Mardi, wanda ya samu raunin harbin bindiga a yayin wani harin fashi da makami ya biya ni N11,000”.

Ya bayyana cewa ya yi tafiya zuwa wasu wurare domin jinyar ’yan fashi, ciki har da wanda aka bayyana da Karanboguwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karamar Hukumar Safana yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Turkiya:Fiye Da’Yan Adawa 300,000 Su Ka Yi Zanga-Zanga Nuna Kin Jinin  Tayyib Ordugan

KAmfanin dillancin labarun “al-Somariyya Newas” ya ambato jagoran ‘yan hamayyar siyasa na kasar Turkiya Uzgor Auzal yana fadin cewa: A daren jiya juma’a adadin wadanda su ka fito Zanga-zangar nuna kin jinin shugaba Rajab Tayyib Urdugan sakamakon sauke da kama ‘yan hamayyar siyasa da ya yi kaga kan mukamansu da su ka hada da magajin garin birnin  Istanbul.

Magajin garin Istanbul Imam Uglu ya yi watsi da duk wata tuhuma da aa yi masa ta hannu a cin hanci da rashawa.

Kamfanin dillancin labaran “Reusters” ya nakalto wata majiyar shari’a tana cewa Imam Uglu ya yi watsi da dukkanin thume-tuhumen da aka yi masa masu alaka a cin hanci da rashawa.

Shi dai Imam Uglu zai tsaya takarar shugabancin kasa da Urdugan, kuma ana tsinkayo cewa zai iya lashe zabe.

Jami’ar adawa da Imam Uglu ya fito daga cikinta “ Turkish Republican Party” ta yi Allawadai da kama Imam Uglu, tare da bayyana shi da cewa, bi ta da kulli ne na siyasa kawai.

Bayan kama Imam Uuglu Zanga-zanga ta barke a cikin birane da garuruwa mabanbanta na kasar ta Turkiya  tare da yin tir da abinda ya faru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno
  • Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu
  • EFCC Ta Cafke Mutum 21 Bisa Zarginsu Da Zambar Intanet A Bauchi
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • Turkiya:Fiye Da’Yan Adawa 300,000 Su Ka Yi Zanga-Zanga Nuna Kin Jinin  Tayyib Ordugan