Aminiya:
2025-03-22@12:52:29 GMT

’Yan Najeriya 52,000 za su sauke farali a 2025

Published: 13th, February 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta tabbatar da cewa an tanadar wa maniyyatan Najeriya 52,000 guraben aikin Hajjin na shekarar 2025.

Wannan na cikin wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktan Bayanai ta NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta fitar.

An kama likita kan laifin yi wa ’yan bindiga magani a Katsina Kwastam ta lalata magungunan biliyan N100 a Ribas

Ta ce hukumar ta riga ta biya kuɗin gurabe 26,287 na maniyyata, sannan ta tanadi wasu 26,000, da za a tabbatar da su gaba ɗaya kafin ranar 13 ga watan Fabrairu, 2025.

Domin cika wa’adin da Hukumar Aikin Hajji da Umrah ta Saudiyya ta bayar, Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya tafi Makka domin ƙulla yarjejeniya.

Ya rattaba hannu kan yarjejeniyar a ranar 17 ga watan Janairu, 2025, bayan tuntuɓar shugabannin hukumar a jihohi da wakilin fadar shugaban ƙasa.

Shugaban ya tabbatar da ƙulla yarjejeniya da waɗanda za su kasance masu hidima tun da wuri don guje wa fuskantar tsaiko.

Wannan matakin yana da muhimmanci saboda ana sa ran fara aikin samar da biza ga maniyyata daga ranar 19 ga watan Fabrairu.

Shugaban NAHCON ya gode wa Mataimakin Shugaban Ƙasa, bisa goyon baya da taimakon da yake bai wa hukumar.

Ya ce hukumar za ta ɗauki matakan da suka dace don tabbatar da cewa maniyyata sun samu damar yin Hajji cikin sauki da kwanciyar hankali.

Ya kuma buƙaci su ci gaba da bibiyar kafofin sadarwa na NAHCON don samun sabbin bayanai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Pakistan Kasar Saudiyya tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho

Ya sanar da cewa, yanzu a Hukumar ana kara samun nada mata kan madafun iko, inda ya sanar da cewa, a yanzu a Hukumar mace ce, ke rike da mukamin Babbar Darakta ta sashen kudi da mulki wato uwargida Bibian C. Richard-Edet.

A cewarsa, a shekarun baya, akalla muna da mata sha biyu da suke rike da mukamain Janar Manaja da kuma mukamain Manajoji a Hukumar

Shugaban ya bayyana cewa, mata na ci gaba da bayar da gudunmawar su wajen habaka fannonin da ke a Hukumar ciki har da bangaren tsaro, kiwon lafiya da sauransu.

“Wadannan wasu misalai ne ‘yan kadan da Hukumar ke yi na inganta ‘yancin mata da tabbatar da ‘yancin su, duba da cewa, bamu iyakance irin kokarin da mata suke da shi ba,” A cewar Dantsoho.

Duk da samar da wadannan ci gaban a Hukumar Dantsoho ya bayyana cewa, Hukumar za ta ci gaba da sauye-sauyen da za su gaba da kare ‘yancin matan da ke aiki a Hukumar.

Kazalika, Dantsoho Hukumar ta NPA za ta ci gaba goyon bayan kare ‘yancin matan da ke aiki a Hukumar da kuma tallafa masu.

“A matsayin mu na Hukumar mun yi alkawarin ba za mu yi kasa a guiwa wajen goyon bayan ‘yancin mata da kuma ‘ya’ya mata da ke aiki a Hukumar, da kuma sauran matan da ba a Hukumar suke yin aiki ba,” Inji Dantsoho.

Dantso ya kuma taya matan da ke aiki a Hukumar murnar zagoyowar ranar ta mata ta duniya, inda ya ba su tabbacin cewa, Hukumar za ta ci gaba da zama a kan gaba wajen samar da damarmaki ga da ‘yan mata da ke a fannin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Tunisiya : Kaïs Saïed, ya kori firaministansa Kamel Madouri
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Taimakon NAMA Don Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Cikin Nasara 
  • Fashewar Tankar Man Fetur: Rundunar ‘Yansanda Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 6, Motoci 14 Sun Kone A Abuja.
  • Jakadan Amurka Ya Ziyarci Sarkin Zazzau Domin Karfafa Alakar Amurka Da Najeriya
  • A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya
  • Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Gwamnan Rikon Kwarya Na Jihar Rivers