Tawagar ta tattaro hukumomi da suka hada da hukumar kula da yanayi (NiMET), hukumar kula da ayyukan ruwa, da hukumar bada agajin gaggawa ta kasa karkashin kulawar ofishin mataimakin shugaban kasa. Wannan yana tare da hadin gwiwar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da ayyukan jin kai (OCHA).

 

A duk duniya, OCHA, wacce ke kula da CERF da Asusun Kula da Ruwa na Kasa (CBPFs) irin su Asusun Ba da Agajin Gaggawa (NHF), tana jagorantar matakai don taimaka wa miliyoyin mutane ta hanyar magance annoba kamar ambaliyar ruwa, fari, da kwalara.

 

A watan Oktoban 2024, CERF ta saki Dala miliyan 5 domin a kara kaimi wajen magance ambaliyar ruwa da kuma magance muhimman bukatu a jihohin Borno da Bauchi a yankin arewa maso gabas da Jihar Sokoto a arewa maso yamma. Kudaden CERF din ya cika dalar Amurka miliyan 6 da hukumar ta NHF ta ware (wanda ya hada da dala miliyan 2 domin daukar matakan da suka dace a dauka tare da yawaitar ambaliyar ruwa da ta raba kimanin mutum 400,000 da muhallansu a Jihar Borno. Ambaliyar ruwa ta lalata abubuwan more rayuwa tare da lalata daruruwan kadada na gonakin noma kafin girbi).

 

A cewar hasashen yanayi na 2025 da NiMET ta gudanar, ana sa ran fara damina a jihohin Arewa irin su Bauchi, Borno, Jigawa, Kano, Katsina, Sokoto, Yobe da Zamfara, tsakanin farkon watan Yuni da Yulin 2025. Wannan lokacin ya zo daidai da lokacin rani (a tsakanin girbi), lokacin da akafi samun karancin abinci sannan kuma farashin abinci mai gina jiki ke kara tashi. Shirye-shirye a kan lokaci game da wadannan abubuwa na da mahimmanci.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno

Aƙalla mutum 11 sun shaƙi iskar ’yanci bayan kuɓuta daga hannun ƙungiyar mayaƙan Boko Haram masu iƙirarin jihadi a Jihar Borno.

Waɗanda suka shaƙi iskar ’yancin na daga cikin mutanen da ƙungiyar Boko Haram ta sace a wani wurin kamun kifi a Doron Baga.

Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram

Wata majiya ta bayyana cewa, wani kwamandan ’yan ta’addan mai suna Tar ne ya jagoranci garkuwa da mutanen ne a ranar 13 ga watan Fabrairu 2025.

Tar da tawagarsa da ke addabar masunta da manoma a gaɓar Tafkin Chadi sun ɗauke mutanen ne yayin da suka afka wa al’ummar Shawaram da ke ƙarƙashin Ƙaramar Hukumar Kukawa ta jihar, inda suka yi awon gaba da mutane 14 da suka haɗa da mata da ƙananan yara.

Wani shugaban al’ummar yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa ’yan ta’addan sun nemi kuɗin fansa jim kaɗan bayan sace su.

Ya bayyana cewa an ceto mutane 11 bayan an biya kuɗin fansa na Naira miliyan 1.4 da wasu al’umma suka tara.

A cewarsa, har yanzu akwai mutane uku da ake garkuwa da su —ciki har da mace guda mahaifinta — a hannun ’yan ta’addan.

Majiyar ta ce mace ta zaɓi ci gaba da zama a hannun ’yan ta’addan saboda sun ƙi sakin mahaifin nata.

Majiyar ta ƙara da cewa Tar ya gindaya sharaɗin cewa muddin ba a biya musu buƙatar sako ragowar mutanen uku ba, zai aurar da macen da ke cikinsu tare da ɗaukar hukunci mai tsanani kan sauran waɗanda ke hannunsa.

Sai dai har zuwa yanzu mahukuntan da wakilinmu ya tuntuɓa ba su ce komai dangane da lamarin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Hajji 2025: Kamfanin Saudiyya zai maka Najeriya a Kotun Duniya
  • Ƴan Ta’adda Sun Sako Manoma 11, Sun Rike 3 A Borno
  • Kasar Sin Ta Taya Mahmoud Ali Youssouf Murnar Zabarsa Da Aka Yi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar AU
  • Jagora : Kokarin Makiya Na Haifar Da Sabani Ya Ci Tura
  • Hukumar Kula Da Ayyukan Duba-gari Ta Kasa Za Ta Karrama Shugaba Tinubu 
  • Yadda Ake Fuf-Fuf