Dogaro Da Kasashen Yamma Ba Zai Tabbatar Da Tsaro A Philippines Ba
Published: 14th, February 2025 GMT
Manyan jami’an Philippines sun sake ikirarin shirin sayen makamai masu linzami dake cin matsakaicin zango na Amurka tare da hada su da batun tekun kudancin Sin. Hakika matakin na Philippines ya damka muradun kasar na tsaro a hannun kawayenta na yammacin duniya.
Dabarar Philippines ta dogaro da kasashen yamma ba za ta samar da tsaro a kasar ba, sai ma akasin hakan.
A daya bangaren, Philippines na yunkurin cin gajiyar tekun kudancin Sin ta hanyar samun goyon baya daga kasashen dake wajen yankin, inda take ci gaba da takala da tada rikici da ma amfani da batun a matsayin wata dama ta jibge makamai masu linzami na Amurka, wanda yake tura yankin tekun kudancin Sin cikin hadari. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
এছাড়াও পড়ুন:
Saree: Filin jirgin saman Ben Gurion ba shi da aminci har sai an kawo karshen yakin Isra’ila a Gaza
Kakakin Rundunar Sojojin Yaman Birgediya Janar Yahya Saree, ya bayyana cewa, Dakarun Yemen sun harba makami mai linzami samfurin Falasdinu-2 a babban filin sauka da tashin jirgin saman Haramtacciyar Kasar Isra’ila na Ben Gurion.
Saree ya jaddada cewa, filin jirgin saman Ben Gurion ba shi da aminci ga zirga-zirgar jiragen sama, yana mai gargadin cewa za su ci gaba da kasancewa a fagen daga har sai Isra’ila ta kawo karshen yakin da take yi a kan al’ummar Gaza.
Tun da farko dai rundunar sojin haramtacciyar kasar Isra’ila ta sanar da cewa, an harba makamai masu linzami a yammacin jiya Juma’a a yankuna da dama da ke tsakiyar Falasdinu da ta mamaye, kuma Isra’ila ta tabbatar da cewa an harbo makaman ne daga kasar Yemen.
An ji karar fashewar wasu makamai masu linzami a sassan tsakiya na Falastinu da Isra’ila ta mamaye da hakan ya hada da kewayen birnin al-Quds. Kafofin yada labaran Isra’ila sun ba da rahoton dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a babban filin jirgin saman Ben Gurion sakamakon wadannan hare-hare na dakarun Yemen.