Dogaro Da Kasashen Yamma Ba Zai Tabbatar Da Tsaro A Philippines Ba
Published: 14th, February 2025 GMT
Manyan jami’an Philippines sun sake ikirarin shirin sayen makamai masu linzami dake cin matsakaicin zango na Amurka tare da hada su da batun tekun kudancin Sin. Hakika matakin na Philippines ya damka muradun kasar na tsaro a hannun kawayenta na yammacin duniya.
Dabarar Philippines ta dogaro da kasashen yamma ba za ta samar da tsaro a kasar ba, sai ma akasin hakan.
A daya bangaren, Philippines na yunkurin cin gajiyar tekun kudancin Sin ta hanyar samun goyon baya daga kasashen dake wajen yankin, inda take ci gaba da takala da tada rikici da ma amfani da batun a matsayin wata dama ta jibge makamai masu linzami na Amurka, wanda yake tura yankin tekun kudancin Sin cikin hadari. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
এছাড়াও পড়ুন:
Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
Ban da haka, yadda gwamnatin Trump ba ta da tabbas a kan manufofinta na haraji yana kuma ba kasashen duniya mamaki. Ba a jima ba da gwamnatin Amurka ta sanar da matakinta na harajin ramuwar gayya a kan kasashen da ke ciniki da ita, sai kuma ga shugaba Trump ya sanar da dage harajin a kan wasu kasashe na kwanaki 90. Kuma kashegari sai aka ji ya yi barazanar cewa, in dai ba a kai ga cimma daidaito a shawarwari ba, to, Amurka za ta maido da harajin. Ban da haka, gwamnatin Amurka ta kuma yi gyara ta ba-zata a kan dokokinta na haraji, inda ta cire harajin ramuwar gayya a kan kayayyakin lataroni da suka hada da wayar salula da kamfuta da sauransu.
Haraji abu ne da ya shafi manufar kasa, amma ga shi gwamnatin Amurka ta mai da shi kamar wasa, wanda hakan ya bayyana rashin tunani na manufofin haraji na kasar, da ma yadda take mai da su a matsayin makamai na nuna fin karfi a duniya. Amurka ta ce wai tana neman tabbatar da yi mata adalci ne, amma a hakika kuwa, tana neman kakaba fifikonta ne a kan sauran kasashe.
Tabbatar da ci gaba hakki ne ga kowace kasa a maimakon wasu kasashe kalilan. Kasashen duniya na rungumar adalci a maimakon nuna fin karfi. Tabbas Amurka za ta cije a yunkurinta na neman tabbatar da fifikonta a kan sauran kasashen duniya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp