Afirka ta Kudu: Ba Za Mu Janye Kararmu Kan Isra’ila A Kotun ICJ Ba
Published: 14th, February 2025 GMT
Afirka ta Kudu ta yi alkawarin ci gaba da shari’ar kisan kiyashi da ta shigar a gaban kotun ICJ a kan Isr’ila, duk da umurnin da Donald Trump ya bayar na katse taimakon da Amurka ke ba kasar Afirka ta Kudu saboda matakin da ta dauka kan babbar kawar Amurka.
“Babu wata dama” kan janye karar ta ICJ, ba tare da la’akari da duk wata barazana ko mataki da Trump zai dauka ba, a cewar ministan harkokin wajen Afirka ta Kudu Ronald Lamola, wanda ya kara da cewa, “Tsayawa a kan ka’idojinmu wani lokaci yana da sakamako, amma mun tsaya tsayin daka kan wannan batu, ganin cewa yana da muhimmanci ga duniya, da kuma bin doka da ka’ida.
Dokar da Trump ya sanya wa hannu ta dakatar da ba da taimako ga Afirka ta Kudu, ya kuma yi alkawarin ci gaba da daukar wasu matakan domin takura kasar Afirka ta kudu kan matakin shigar da kara da ta dauka a kan Isra’ila game da batun yakin Gaza.
Afirka ta Kudu ta gabatar da karar kisan kiyashi kan “Isra’ila” a karshen shekara ta 2023 zuwa kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, inda ta bukaci kotun kasa da kasa da ta dauki matakai kan mahukuntan Isra’ila saboda karya yarjejeniyar kisan kare dangi ta Majalisar Dinkin Duniya.
Ireland a hukumance ta shiga cikin shari’ar Afirka ta Kudu a watan Disamba 2024, kuma jim kadan bayan haka, Cuba ta sanar da aniyar ta na shiga cikin lamarin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
Martanin da Fadar Shugaban Kasar ta mayar, ya biyo bayan nuna damuwa a kan matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta dauka na amincewa da takunkumin da aka kakaba wa Nijeriya, bisa zargin kashe Kiristoci.
Da yake goyan bayan wannan matsaya, Shugaban Kungiyar Kiristoci ta Kasa (CAN) reshen Arewa, Rabaran Yakubu Pam ya bayyana a baya bayan nan cewa, abubuwan da suke faruwa na musgunawa Kiristoci, su yi matukar raguwa.
Har ila yau, ya bayyana ci gaban da aka samu, musamman a bangaren wariya ko nuna banbanci ga Kiristoci, wajen mallakar filaye; domin gina Coci-coci da kuma batun tilasta barin addinin da kuma aurar da yara ‘yan mata Kiristoci.
Kazalika, gwamnati ta sake nanata kudirinta na ci gaba da karfafa addinai tare da ba su muhimmanci, inda kuma ta bukaci kungiyoyin kasa da kasa da su yi la’akari da abubuwan da suke faruwa yanzu, maimakon rika dogaro da rahotannin da suka riga suka gabata.
Haka zalika, wata sanarwa da mukaddashin mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ta sanar da LEADERSHIP; ta bayyana damuwarta kan yadda ake faman yada labaran karya da kuma rahotannin bata-gari, dangane da kashe-kashen da ake yi wa Kiristoci a Nijeriya.
“Wadannan rahotannin karya da shaci fadi, na ci gaba da yin tasiri ga gwamnatocin kasashen waje, musamman ma Gwamnatin Amurka; don ayyana Nijeriya a matsayin kasa mai cin zarafin Kiristoci.
Don haka, Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar, ta bukaci kasashen duniya da su yi taka-tsan-tsan tare da rika tantance bayanai, kafin su kai ga yanke hukunci ko yin kalaman da ka iya tayar da rikici a Nijeriya. “Muna kira ga masu ruwa da tsaki, ciki har da kafafen yada labarai, kungiyin al’umma da kuma abokan huldar kasashen waje; su guji yada labaran da ba su da tabbas a kansu, wadanda za su iya gurgunta zaman lafiya da hadin kan ‘yan kasa”, in ji Ebienfa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp