HausaTv:
2025-02-20@09:14:12 GMT

Pezeshkian: Iran za ta magance matsalolinta ne ta hanyar  dogaro da kanta

Published: 14th, February 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi gargadin cewa makiya kasarsa suna neman murkushe al’ummar kasar  ta hanyar takunkumi da barazana.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ta yi da masana da masu fada aji na lardin Bushehr da ke kudancin kasar a ranar Alhamis , inda ya ce “Makiya suna son mu ulakanta a gabansu ta hanyar takunkumi da barazana, amma ba za mu yi kasa a gwiwa ba, kuma za mu magance matsalolinmu ta hanyar dogaro da jama’a.

Ya yi kakkausar suka kan irin matakan da Amurka ke dauka a kan Iran wadanda suke karo da juna, yana mai cewa shugaban Amurka Donald Trump na ikirarin cewa yana son tattaunawa da Iran amma a lokaci guda ya kakabawa Tehran takunkumi mafi tsauri.

“Ba ma son wani ya sanya mana takunkumi,” in ji Pezeshkian, ya kara da cewa, “Ba wai idan Amurka ta kakaba mana takunkumi ba, ba za mu iya yin komai ba. Za mu tafiyar da kasar ta hanyar dogaro da karfin cikin gida.”in ji Pezeshkian.

Ya nanata manufofin Iran na yin mu’amala da dukkan kasashe cikin lumana da ‘yan uwantaka, yana mai jaddada cewa, “Muna kokarin kulla kyakkyawar alaka da abokantaka da makwabta.”

Shugaban ya kara da cewa hadin kai, mu’amala da tsare-tsare na taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalolin cikin gida.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri

Kakakin ma’aikatan shari’a a kasar Iran ya bayyana cewa jami’an tsaro na kasar Iran sun kama mutane biyu yan kasar Burtaniya tare da tuhumar aikin liken asiri a lardin Kerman na kasa.

Kamfanin dillancin labaran (IP) na kasar Iran ya bayyana cewa mutanen biyu suna tafiye-tafiye zuwa lardunan kasar Iran suna tattara bayanai a cikin watan Jeneru na wannan shekarar a lokacinda suka fada hannun Jami’an tsaron kasar.

Labaran sun kara da cewa mutanen biyu sun sauya kamamnci, zuwa kamar masu yawon bude ido suna tsammanin cewa ba za’a ganesu ba.

Kakakin ma’aikatar Shari’ar ya bayyana cewa ma’aikatan liken asirin kasashen turai da dama sun fi aiki ne a bangaren karatu a makarantun kasar Iran.

Asghar Jahangir ya bayyana cewa wadannin yan liken asiri daga kasar Burtania, suna aikin leken asirin su ne da sunan bincike a wata Jami’a a cikin kasar, amma duk lokavinda suka fito sais u aikawa cibiyoyinsu a kasashen yamma da sakonni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Mususlunci A Iran IRGC Sun Bada Sanarwan Kai Hari A Kan HKI Karo Na Uku
  • Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Ga Tattaunawar Amurka Da Rasha Kan Rikicin Ukraine
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Irin Gagarumar Rawar Da Iran Ta Taka A Fegen Tsaro Yakin Tekun Pasha
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Ministan Harkokin Waje Iran Ya Jaddada Cewa Iran Ba Zata Tattauna Da Amurka A Karkashin Takunkumai ba
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • Kasar Sin: Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba Wajen Kartar Kasashe Masu Karfin Iko Ba Ne
  • Iran: Himmati Yana Halattar Taro Dangane Da Matsalolin Da Suka Addabar Kasashe Masu Tasuwa
  • HKI Ba Zata Yarda A Kafa Kasar Palasdinu Ba, Saboda Barazana Ce Ga Wanzuwar HKI