Ana nuna damuwa akan karancin kayan gwajin HIV a Taraba
Published: 14th, February 2025 GMT
Kungiyoyin farar hula masu yaki da zazzabin cizon sauro, rigakafi da abinci mai gina jiki (ACOMIN), reshen jihar Taraba, ta koka kan matsalar karancin kayan gwajin cutar kanjamau a jihar.
Shugaban kungiyar na jiha, Alhaji Muhammad Danburam ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar wayar da kan hukumar yaki da cutar kanjamau ta Taraba (TACA), ofishin kula da magunguna masu muhimmanci, da gidauniyar REDAID Nigeria Foundation.
Danburam ya bayyana cewa, wani bincike da aka yi kwanan nan a wasu cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 18 a kananan hukumomin Ardo-kola, Bali, da Takum, ya nuna cewa kayan gwajin cutar kanjamau sun kare a cibiyoyin.
“Rashin kayan gwajin zai kawo cikas ga kokarin yaki da yaduwar cutar kanjamau a jihar,” in ji Danburam.
Ya yi kira ga gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki da su dauki matakin gaggawa don magance karancin.
A jawabinsa, Ko’odinetan Sashen Gudanar da Dabaru (LMCU) na Jiha, Pharm. Pinkai Bade, ya bukaci ‘yan kasar da su jajirce wajen tabbatar da samar da wadannan kayyakin tare da bayyana cewa tsarin samar da kayayyaki na da matukar kalubale sakamakon dakatar da tallafin da Amurka ke ba Najeriya.
Ya kuma yi nuni da cewa, Nijeriya ta himmatu wajen ganin an cike gibin da ke tattare da cutar kanjamau da kuma cimma nasarar rigakafin kamuwa da cutar daga uwa zuwa yara (PMTCT) nan da shekarar 2030.
Hukumar kula da fasaha ta REDAID ta Najeriya, Mista Stanley Nfor, da sakataren hukumar yaki da cutar kanjamau ta Taraba (TACA), Mista Bala Zugyeri, sun bayyana cewa, masu hannu da shuni kadai ba za su iya biyan bukatar kayayyakin gwaji da sauran muhimman kayayyaki ba, inda suka jaddada bukatar tallafin gwamnati.
Karshe/Jamila Abba/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Taraba cutar kanjamau kayan gwajin
এছাড়াও পড়ুন:
An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
Jami’an tsaro sun kwace miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai Naira miliyan 300 sannan ta kama mutane 650 da ake zargi a Jihar Kano.
Kwamitin Dawo da Zaman Lafiya da Kyautata Dabi’un Matasa ta Jihar Kano ce ta yi wanna kame a fadin jihar, kamar yadad ta bayyana a rahotonta.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Bakori, ya bayyana, ya bayana cewa mutum 150 daga ckin adadin an kama su ne kan laifukan dabanci da kwacen wayada da dangoginsu.
Kwamitin ya ce aikin haɗin gwiwar, ya yi wannan nasara ne bayan da suka kai samame a kan maboyar masu aikata laifuka da aka gano a kananan hukumomi takwas da ke garin Kano.
An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken TinubuHukumar ta bayyana cewa an gudanar da aikin ne tare da ’yan sanda da Hukumar Yaki da Miyagun Kwayoyi (NDLEA) da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (NSCDC) da Hukumar Kula da Gidajen Yari da Hukumar Shige da Fice, da sauran hukumomi.
Da yake jawabi a wani taro da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, Shugaban Rundunar, Dakta Yusuf Ibrahim, ya ce ƙwace miyagun ƙwayoyin da aka kiyasta kimarsu a Naira miliyan 300 zai taka muhimmiyar rawa.
Ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da tallafin al’umma ke takawa wajen dorewar ƙoƙarin Rundunar na inganta tsaron jama’a.
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdussalam, ya yaba wa nasarorin da Rundunar ta samu, yana mai tabbatar da kudurin gwamnatin jihar na magance ƙalubalen tsaro ta hanyar irin waɗannan matakai masu ƙarfi. Sa’annan ya jaddada buƙatar haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da al’umma don samun ɗorewar tsaro.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, ya yaba da ingancin ayyukan da aka gudanar bisa ga bayanan sirri, yana amai kira da a kafa wata kotu ta musamman domin hanzarta shari’ar waɗannan laifuka.
Kwamandan Hukumar NDLEA na Jihar, Abubakar Idris, ya yaba da haɗin gwiwar da ke tsakanin hukumomin tsaro kuma ya yi kira da a ci gaba da shidon magance matsalolin tsaro a Jihar Kano.