Sharhi Kan Dabarun Noman Dabino A Nijeriya
Published: 14th, February 2025 GMT
Duk da cewa, ana kara samun yin nomansa da yawa, ana kuma ci gaba da samun karancinsa, musamman saboda yadda al’umma ke kara bukatarsa.
Kamar Ban Ruwa Nawa Bishiyar Dabino Ke Bukata?
Dabinon da aka shuka, bai cika bukatar a dinga yi masa ban ruwa bayan an shuka shi ba, musamman a lokacin kakar damina.
A Wane Yanayi Dabino Yake Girma?
Dabino ya fi yin girma a yanayin zafi, haka nan kuma ya fi yin kyau a kasar noma ta kasar Amurka da ake samun rana mai zafi.
Kamar Zufin Rami Nawa Dabino Ke Bukata?
Yana girma a zurfin ramin da ya kai kafa daya zuwa kafa sha daya tare kuma da santi mita daga talatin zuwa arba’in da biyar, wannan ya danganta da irin ingancin kasar noman da aka shuka shi da kuma irin yanayin, haka nan; yana kai wa daga tsawon shekara 15 zuwa 20 kafin ya kammala girma.
A duk fannin duniya, Nijeriya ce kawai ke nomansa sau biyu a shekara, har Nahiyar Afirka ta Arewa da Gabas ta tsakiya, inda ake hasashen Dabinon ya samu asali, sannan ana yin nomansa ne a kakar noma daya.
Dabinon da aka shuka, na fara fitar da fure ne daga watan Janairu zuwa watan Fabirairu, inda kuma yake kammala nuna daga watan Yuni zuwa watan Oktoba.
Wanda kuma aka shuka a kakar noman damina, yana fara yin fure ne daga watan Satumba zuwa watan Oktoba, inda kuma yake kai wa munzalin a girbe shi daga watan Fabirairu zuwa watan Maris.
Batun Shuka Shi:
Ana amfani da Iri don shuka shi ko kuma a shuka Saiwarsa wacce ke girma zuwa Bishiya.
Ana kuma yanko Saiwar ce daga jikin Bishiyar da ta kai daga shekara hudu zuwa biyar, inda kuma ake fara shuka shi daga watan Juli zuwa watan Satumba, haka a kadada daya ana iya samun Bishiyar Dabino kimanin 150.
Gyaran Gona:
Ana so a gyra gonar da za a shuka Dabino kafin ruwan damina ya fara sauka, inda ake so a yi wa gonar haro; domin ta samu danshi sosai.
Zuba Taki:
An fi so a zuba masa takin gargajiya da ke dauke da sindarin ‘Nitrogen’, musamman domin ya yi saurin girma.
Ban Ruwa:
Bishiyar Dabino na jurewa kowane irin yanayi na noma, an fi so a yi masa ban ruwa, musamman a lokacin rani.
Cire Ciyawa:
Ana bukatar manomi ya tabatar ya kiyaye wajen yin noma, musamman don gudun kada ya kamu da cututtuka ko harbin kwari.
Lokacin Yin Girbi:
Ana yi masa girbi ne bayan ya kammala girman baki-daya, wato daga shekara 15 zuwa shekara 20.
Adana Shi Bayan Girbi:
Sabon Dabinon da aka girbe, ana adana shi a cikin na’ura mai sanyi daga sati biyu zuwa uku, ana kuma iya adana shi har zuwa tsawon wata hudu.
Hada-hadar Kasuwancinsa:
Dabino ne yake tallan kansa da kansa, musamman ganin cewa, jama’a na kara bukatarsa, kana ana sarrafa shi zuwa nau’ikan wasu abin sha; kamar kunun Aya da sauran makamantansu.
Daga Tsawon Kafa Nawa Bishiyar Dabino Ke Girma?
Bishiyar Dabino na kai wa tsawon kafa 20, banda ganyensa; yana kuma kai wa tsawon shekara daga 15 zuwa 20 kafin ya kammala girman.
Har ila yau, Dabinon da ya kai tsawon shekara 100, yana iya kai wa tsawon kafa 100.
Ana Samun dimbin Riba A Noman Dabino
A shekarar 2020, Kalifoniya ta samar da tan 49,300 da aka noma kadada 12,500, inda kuma a duk kadada daya aka noma tan 3.94 da kudinsa ya kai dala 2,320 na kowane tan daya. An kuma kiyasta yawan amfanin Dabinon da cewa; ya kai dala miliyan 114.
কীওয়ার্ড: Bishiyar Dabino Bishiyar da
এছাড়াও পড়ুন:
USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram
Gwamnatin Amurka ta ƙudiri aniyar gudanar da bincike kan yadda gwamnatocin da suka gabata suka riƙa sarrafa kuɗaɗen da aka fitar domin bai wa Nijeriya da wasu ƙasashen tallafi.
Hakan dai ya biyo bayan matakin da Shugaban Amurkan, Donald Trump ya ɗauka a watan Janairu na dakatar da duk wani tallafi da Amurkan ke bayarwa a ƙetare har na tsawon kwanaki 90.
DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi Majalisa ta tsayar da ranar sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin Dokar HarajiShugaba Trump ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta gudanar da binciken ne a dalilin ruɗanin da ya dabaibaye duniya wanda ke cin karo da muradun Amurkan.
Haka kuma, Shugaba Trump ya ce za a gudanar da binciken ne domin amsa kiraye-kirayen ke yi wajen bitar ayyukan da Hukumar Bayar da Agaji ta USAID.
A bayan nan ne wani ɗan Majalisar Dokokin Amurka, Scott Perry, ya bayyana cewa hukumar raya kasashe ta Amurka (USAID) ke samar da kuɗaɗe ga kungiyoyin ’yan ta’adda, ciki har da Boko Haram.
Perry ya yi wannan iƙirarin ne yayin zaman sauraron rahoton kwamitin majalisar a kan yadda hukumomin gwamnatin Amurka ke aiwatar da ayyuka da sarrafa kuɗaɗe a ranar Alhamis ta makon jiya.
Zaman mai taken “yaki da barna: Kawar Da Annobar Almundahana Da Zamba,” ya maida hankali ne a kan zargin barnatar da kudaden masu biyan haraji.
“Waye ke samun wani banagare na kudaden? ko wani a ɗakin nan ya kiyaye waɗannan sunaye? saboda kudadenku, dala miliyan 697 a duk shekara, baya ga aika ƙarin kuɗaɗe ga Madrasas da ISIS da Al-Qa’ida da Boko Haram da ISIS Khorasan da sansanonin horas da ‘yan ta’adda. Wadannan su ne abubuwan da take daukar nauyi,” kamar yadda Perry ya bayyana.
Shafin yanar gizon kwamitin ya bayyana cewar zai yi aiki tare da ma’aikatar bin diddigin ayyukan hukumomin gwamnatin Shugaba Trump domin magance barna, da dakile almundahana tare da gudanar da cikakken bincike a kan yadda aka zambaci masu biyan harajin Amurka.
Ƙungiyar Boko Haram, wacce aka sani da Jamā’at Ahl as-Sunnah lid-Da’wah wa’l-Jihād, ƙungiya ce ta ‘yan ta’adda da ta ayyana kanta a matsayin mai tayar da ƙayar baya yankin arewa maso gabashin Nijeriya, da kuma ƙasashen Chadi, Nijar, Kamaru da kuma Mali.
Ƙungiyar ta shafe sama da shekaru 15 tana tashe-tashen hankula a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya, inda ta kashe dubun-dubatar mutane, a hare-haren da take kai wa ’yan sanda, da sojoji da fararen hula.
Zan gabatar da ƙudiri… — NdumeA kwanan ne shi ma Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu ya buƙaci gwamnatin Nijeriya ta gaggauta gudanar da bincike kan iƙirarin da ɗan majalisar dokokin Amurka ya yi na cewa hukumar USAID da gwamnatin Trump ta rufe ta tallafa wa ƙungiyoyin ta’addanci da suka haɗa har da Boko Haram a ƙasar.
Ndume ya ce ba batu ba ne da ya kamata gwamnatin Nijeriya ta naɗe hannunta, la’akari da girman barnar Boko Haram a Jihar Borno.
Ya ce zai gabatar da ƙudiri kan binciken zargin ɗan majalisar dokokin na Amurka.
“In an tashi binciken za mu yi tambayoyi, saboda haka za mu bincika domin mu ’yan Nijeriya da abun ya shafa ya kamata mu sa ido don a san matakan da za a ɗauka, saboda ba ƙaramin ɓarna Boko Haram suka yi mana ba,” in ji Ndume.
BBC ya ruwaito Sanata Ndume yana zargin cewa USAID ba ta aiki tare da hukumomin da ya kamata ta yi aiki tare da su a Nijeriya, lamarin da ya ke dasa ayar tambaya.
“Ba sa bari jami’an tsaronmu su sanya ido kan abubuwan da suke yi ballantana su ba da shawara.”
An dai ƙirƙiri Hukumar USAID a shekarun 1960 domin taimaka wa ayyukan agaji a madadin gwamnatin Amurka a kowanne yanki na duniya.
Tana da ma’aikata dubu 10, wanda kashi biyu bisa uku na aiki a ƙetare. Tana da cibiyoyi a sama da ƙasashe 60, sannan tana ayyuka daban-daban a sauran ƙasashe.
Sai dai galibin ayyukanta wasu ƙungiyoyin take bai wa kuɗi su aiwatar, nata shi ne sa ido da tabbatar da cewa an kashe kuɗaɗen bisa tsari.
Ayyukanta na da dimbin yawa. Misali, USAID ba tallafin abinci kaɗai take bayarwa a ƙasashe masu fama da yunwa ba, tana kuma aiki wajen gane inda za a fuskanci fari, da kuma inda za a buƙaci agajin gaggawa na yiwuwar ƙarancin abinci a nan gaba.
Galibin kasafin kuɗin USAID ana kashe su ne a fannin lafiya, irin su rigakafin Polio a ƙasashen da cutar ke yaɗuwa da kuma taimakawa wajen daƙile yaduwar cututtuka da ake yi wa kallon annoba.