Aminiya:
2025-03-25@15:05:01 GMT

Fursunoni 3 sun lashe Gasar Al-Ƙur’ani a Kano

Published: 14th, February 2025 GMT

Wasu fursunoni uku da ke tsare a gidajen yari daban-daban sun lashe Gasar Musabakar Al-Kur’ani da aka gudanar a Jihar Kano.

Fursunoni sun lashe gasar da Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Jihar Kano ta shinrya a matsayin wani bangare na tsarin ilimin fursunoni.

An shirya musabakar ce da nufin sauya tunanin fursunoni domin su zamo mutane da al’umma za ta amfana da su bayan sun kammala zaman gidan yari.

Mai magana da yawun hukumar gidajen yari a Jihar Kano, CSC Musbahu Lawan Kofar Nasarawa, ya ce an shirya musabakar ce domin kyautata halayyar masu zaman gidan yari.

Tirela ta murƙushe mutane a Gadar Hotoro a Kano Gwagwarmayar Ahmadu Haruna Zago, Bakaniken Jam’iyya

Ya bayyana cewa furunan da ya lashe gasar yana tsare ne a gidan yarin Kumawa, inda ya samu kyautar Naira dubu dari.

Na biyu kuma a Gidan Yarin Goron Dutse yake tsare, kuma shi ma ya samu kyautar Naira dubu 50.

Mutum uku yana tsare ne a Gidan Yarin da ke Janguza kuma ya samu kyautar Naira dubu ashirirn.

Da yake jawabi a wurin taron, Shugaban Kungiyar Alarammomi, Gwani Shuaibu Shehu, ya yaba wa Kwamnturolan Hukumar Gidajen Yari na Jihar Kano kan zurfin tunaninsa wajen shirya musabakar.

Ya kuma yaba masa da sama wa tsararrun wuraren da suka dace domin gudanar da al’amuran addini da sauran abubuwan da za su inganta rayuwarsu.

Gwani Shuaibu ya kuam yaba wa Ko’odinentan hukumar kan harkokin addinin, DSC Murtala Nasidi Kabara bisa yadda suke koyar da fursunonin karatun Al-Kur’ani..

A nasa jawabin, Kwanturolan hukumar, Ado Inuwa ya bayayan godiyarsa ga Sarkin Kano Muhammadu Sunusi II bisa halartar gasar musabakar da kansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gidajen yari Gidan Yari a Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa

A cewarsa, domin tabbatar da gudanar da wannan tantancewar, an samar da kwakkwaran kwamitoci a matakin jiha da kananan hukumomi tare da sauran sassan hukumomin da ke da alaka da kudi, sannan an ba su umarni samar da dukkan bayanan biyan albashin nan take.

Farouk ya bukaci ma’aikatan da matsala ta shafa su kai kansu gaban hukumominsu tare da nagartattun bayansu kan dalilin kin bin wannan umarni, saboda a kula da sabunta kundin biyan albashin.

Ya ce Mambobin kwamitin sun hada da manyan sakatarorin daga manyan ma’aikatu, wakilai daga kwamitin tsara jadawalin albashi da kuma wasu manyan jami’an a ofishin sakataren gwamnatin Jihar Kano. Sannan ya jadadda cewa bin wannan umarni ya zama wajibi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi
  • Juventus ta sallami kocinta Thiago Motta
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • An shiga ruɗani yayin da Sanusi II da Bayero ke shirin hawan salla a Kano
  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa