Aminiya:
2025-04-14@16:46:06 GMT

Ta kacame tsakanin mahaifiyar 2Face da budurwarsa

Published: 14th, February 2025 GMT

Hakan dai ya faru ne dalilin baiko da fitaccen mawaƙin ya yi da ’yar majalisar jiha mai wakiltar Egor a jihar Edo, Natasha Osawuru, a wani bidiyo da ya karaɗe soshiyal midiya.

Ɓullar bidiyon ke da wuya mahaifiyar 2Face, Rose Idibia, ta fito a wani bidiyo tana roƙon duk wata uwa ta taya ta roƙon ‘yar majalisar ta karya asirin da ta yi wa ɗanta.

Kalaman mahaifiyar tasa dai na da nasaba da rabuwar 2Face da matarsa Annie da har yanzu bai kammala ba a hukumance.

Mahaifiyar tasa ta ce rashin haƙurin jiran aurensa ya rabu da tsohuwar matar tasa, da gaggawar neman auren ‘yar majalisar ne ya sanya ta gano cewa ɗan nata ba a hayyacinsa ya ke ba.

Tirela ta murƙushe mutane a Gadar Hotoro a Kano Masu noman tabar wiwi na barazanar ƙona gidajenmu —Makiyaya

Tun kafin auren 2Face da Annie wacce tsohuwar jarumar Nollywood ce sun sha yamutsa hazo, musamman haife-haife da 2Face ɗin ya yi da wasu matan biyu, duk da cewa suna tsaka da soyayya a lokacin.

Kazalika bayan auren rahoton soyayya da wasu matan bai tsaya ba, baya ga rigingimu tsakanin danginsa da Annie, da kuma zargin da ɗan uwanta ya yi mata na jefa shi a hanyar shaye-shaye.

Rahotanni dai na nuna sai da 2Face ya haifi ‘ya’ya huɗu da wasu matan kafin su yi aure, sannan suka haifi na biyar ɗin tare.
Idan za a iya tunawa dai, makonni da suka gabata ne 2Face ɗin ya fito ya ce zai rabu da tsohuwar matarsa Annie baya shekaru 12 da aure.

Sai dai daga baya ya fito ya ce masu kutse ne suka aikata hakan, bayan abokanan aikinsa da dama sun fito sun yi Alla-wadai da fito da zancen soshiyal midiya.

Kwanaki kaɗan bayan nan ne kuma ya sake yin bidiyo ya ce babu wani kutse da aka yi wa shafinsa, shi ne ya rubuta da kansa.
Jaridar Punch ta rawaito tsohuwar matar 2Face ɗin na wani wurin gyaran hali yanzu haka saboda fama da matsanancin shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da ta ke yi, kuma fitacciyar mawaƙiya Tiwa Savage na daga cikin masu kula da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Natasha Osawuru Nollywood

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano

Rundunar ‘yansandan Nijeriya ta gano wani haramtaccen wurin hada makamai a jihar Kano, lamarin da ya kai ga kama wasu mutane uku tare da kwato bindigogi kirar gida guda 15 tare da harsashi 102. Wadanda ake zargin sun hada da Abdul Sadiq mai shekaru 43; Ahmad Muazu, 22; da Aliyu Sharif, mai shekaru 40, an kama su ne a ranar 10 ga watan Afrilu a unguwar Dorayi Babba da ke jihar, sakamakon wani hadin gwiwa da jami’an rundunar ‘yansandan jihar Kano suka jagoranta. Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna  Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan, ACP Olumuyiwa Adejobi ya tabbatar da kamen a wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce an gudanar da aikin ne bisa wani sahihan bayanai da suka kai ga gano tarin haramtattun makaman. Sufeto-Janar na ‘yansanda, IGP Kayode Egbetokun, ya yaba da matakin gaggawar da jami’an suka dauka tare da jaddada aniyar rundunar na dakile yaduwar makamai marasa lasisi a fadin kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Xi Da Prabowo Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Indonesiya
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • Sin Za Ta Kara Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar Zuwa 125%