Leadership News Hausa:
2025-03-25@15:05:01 GMT

Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Jahohi 31 Ya Jawo Cece-kuce A Nijeriya

Published: 14th, February 2025 GMT

Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Jahohi 31 Ya Jawo Cece-kuce A Nijeriya

Sannan a kudu maso kudu, masu goyon bayan sabbin jihohi suna son a samar da jihohin Ogoja, Warri, da Bori daga jihohin Kuros Ribas, Delta da Ribas, da kuma Jihar Obolo daga jihohin Ribers da Akwa Ibom na yanzu.

Daga kudu maso yamma kuwa, akwai shawarwarin samar da sabbin jihohi shida. Jihohin da ake shirin kirkira sun hada da Toru-ebe da za a sassaka daga jihohin Delta da Edo da Ondo na yanzu, da kuma jihohin Ibadan da Lagoon da za a sassaka daga jihohin Oyo da Legas, bi da bi.

Sauran sun hada da Jihar Ijebu da za a samar daga Jihar Ogun ta yanzu da kuma jihohin Oke-Ogun da Ife-Ijesha da za a kirkiro daga jihohin Ogu da Oyo da Osun na yanzu.

Kwamitin majalisar kan sake fasalin kundin tsarin mulkin kasar nan, a wata sanarwa da ya aike wa mambobin majalisar wakilai, mai dauke da sa hannun mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin, ya umurci masu goyon bayan kirkiro sabbin jihohin da su sake gabatar da bukatarsu kamar yadda sashe na 8 (1) na kundin tsarin mulkin 1999 ya tanada.

“Kwamitin ya duba shawarwarin samar da sabbin jihohi kamar yadda sashe na 8(1) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 ya tanada. Wannan sashe ya zayyana takamaiman bukatu wadanda dole ne a cika su don fara aikin kirkirar sabbin jihohi. Za a sake gabatar da shawarwari bisa la’akari da wadannan sharudda,” in ji Kalu.

Wasu ‘yan Nijeriya dai sun soki matakin, suna masu cewa abin da ya kamata shugabanni su mayar da hankali a kai shi ne, yadda za a mayar da kasar mulkin yanki ba wai samar da karin jihohi ba.

Masu yada wannan labari na ganin cewa Nijeriya ta fi samun shugabanci nagari a lokacin da ake tsarin milkin yankuna, lura da cewa samar da jihohi 12 daga yankuna hudu da gwamnatin mulkin soja ta Janar Yakubu Gowon ta yi ba don wani ci gaba ba ne, sai dai wani yunkuri ne na raunana yankin gabas a lokacin yakin Biafara.

Amma, akwai wadanda kuma suka yi jayayya cewa samar da jihohi yana kawo ci gaba ga mutanen da ke ganin an ware su kuma za su yi maraba da shawarwarin muddin sun bi ka’idojin kamar yadda ‘yan majalisar suka sake nanata a baya.

Haka kuma, akwai wasu da ba su yarda da samar da karin jihohi a Nijeriya gaba daya ba, amma suna da ra’ayin cewa a yi adalci a kara wa yankin kudu maso gabas karin jiha daya domin daidaita yankin da takwarorinsa.

kungiyoyin yankin biyu da suka yi kaurin suna wajen nuna adawa da matakin sun hada da kungiyar kabilar Yarbawa ta Afenifere da kuma kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF). Dukkan bangarorin biyu sun bayyana shirin samar da jihar a matsayin abin dariya kuma ba amshesshe ba ne.

Sai dai kungiyar ta Afenifere ta bukaci majalisar dokokin kasar da ta mayar da hankali kan sauye-sauyen kundin tsarin mulkin kasar da zai raba madafun iko, da maido da albarkatun kasa a yankunan, da kuma bai wa jihohi ‘yancin cin gashin kansu domin su bunkasa cikin hanzari.

Haka zalika, kungiyar tuntuba ta Arewa, ta kuma bayyana rashin amincewarta da shirin samar da sabbin jihohi 31, inda ta bayyana ra’ayin a matsayin wanda bai kamata ba.

Amma, babbar kungiyar kare al’adun Igbo, Ohanaeze Ndigbo ta bi wata hanya ta daban. Tana da ra’ayin cewa a kara wa yankin kudu maso gabas sabbin jihohi domin magance kura-kuran da aka yi wa yankin dangane da batun samar da jihohi.

A nasa bangaren, Babban Lauyan Nijeriya kuma Farfesa a fannin shari’a, Cif Mike Ozekhome, ya bayyana hakan a matsayin almubazzaranci.

Shima da yake magana game da damuwar da ‘yan Nijeriya da dama ke da shi dangane da yadda ake tada zaune tsaye na samar da sabbin jihohi, Mista Osita Okechukwu, tsohon Darakta Janar na Muryar Nijeriya ya yaba da matakin a matsayin kyakkyawan misali ga hadin kan kasa.

Najeeb Bello ya kasa boye bacin ransa game da lmarin, inda ya ce, “Me zai hana smar da jihohi 311? A bari kowace karamar hukuma a Nijeriya ta zama jiha kawai.”

Bashir Ahmad yana goyan bayan samar da sabbin jihohi, amma ya bayar da shawara a kara karkasa Jihar Kano duba da yawan al’ummar da take da shi.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: samar da sabbin jihohi kundin tsarin mulkin samar da jihohi

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Apple Ya Sanar Da Zuba Sabon Jari A Fannin Samar Da Makamashi Mai Tsafta A Sin

Babban kamfanin fasahar nan na Amurka wato Apple, ya sanar da shirinsa na zuba jarin da ya kai kudin Sin yuan miliyan 720, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 100.31, a fannin samar da makamashi mai tsafta da ake iya sabunta amfani da shi a kasar Sin.

Wata sanarwa da kamfanin ya fitar a Litinin din nan, ta ce kudaden jarin za su samar da damar kara yawan megawatt duk sa’a kusan 550,000 na lantarkin da ake samarwa ta iska, da hasken rana duk shekara, cikin jimillar lantarkin kasar Sin, adadin da kuma ake fatan karuwarsa yayin da masu zuba jari suka karu.

Kazalika, sanarwar ta hakaito babban jami’in gudanarwa na kamfanin Jeff Williams, na cewa yanzu haka masu samarwa kamfanin Apple kayayyakin harhada hajojinsa a kasar Sin na kan gaba wajen samar da ci gaban fasahohi masu nasaba da na’urori masu kwakwalwa, da fannin makamashi mai tsafta.

Williams ya kara da cewa, sakamakon kaddamar da kudaden jarin na wannan karo, kamfanin Apple na fatan kara zurfafa hadin gwiwarsa da sassan masu samar masa da kayayyaki na Sin, ta yadda za a kai ga ingiza kirkire-kirkire domin cin gajiyar dukkanin duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Yari A Libya – Gwamnati
  • Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru
  • An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • An Ɗauko Sojoji Daga Wajen Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  •  Syria: Isra’ila Ta Kai Hari A Kan Sansanin Soja A Yankin Dar’a
  • Kamfanin Apple Ya Sanar Da Zuba Sabon Jari A Fannin Samar Da Makamashi Mai Tsafta A Sin
  • Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — Zulum
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024