Aminiya:
2025-03-25@14:00:22 GMT

Shugaban Ƙungiyar Afenifere, Adebanjo ya rasu

Published: 14th, February 2025 GMT

Shugaban Kungiyar Yarbawa zalla ta Afenifere, Pa Ayodele Adebanjo ya rasu yana da shekara 96.

Rahotanni sun ce dattijon ya rasu ne da safiyar Juma’a a gidansa da ke Lekki a Jihar Legas. An tabbatar da rasuwarsa a wata sanarwa da iyalansa suka fitar.

Fursunoni 3 sun lashe Gasar Al-Ƙur’ani a Kano Ta kacame tsakanin mahaifiyar 2Face da budurwarsa

“Ya rasu a safiyar yau Juma’a, 14 ga Fabrairu, 2025, a gidansa da ke Lekki, a Legas Nijeriya yana da shekara 96.

Za mu ci gaba da riƙe alƙawarinsa na fafutukar tabbatar da gaskiya da adalci.

Sanarwar ta ƙara da cewa, har zuwa ƙarshen rayuwarsa ya yi ta bayyana halayansa da gwagwarmayar na tabbatar da samun ’yanci da ci gaban Najeriya gaba ɗaya.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannu a madadin iyalan Madam Ayotunde Atteh (nee Ayo-Adebanjo), Madam Adeola Azeez (nee Ayo-Adebanjo), da Mista Obafemi Ayo-Adebanjo.

Shahararren Lauya, tsohon sakataren Ƙungiyar Action Group kuma shugaban Ƙungiyar Afenifere na Ƙasa, Adebanjo ya rasu ya bar matarsa, Cif Christy Ayo-Adebanjo da ’ya’ya, jikoki da ’ya’yan jikoki.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa

Kimanin shekaru 12 da suka wuce, wato a ranar 23 ga watan Maris din shekarar 2013, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya, a karon farko, yayin da yake jawabi a wata jami’a dake birnin Moscow na kasar Rasha. Asalin tunanin ya shafi al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya bukaci a samu jituwa, da daidaito tsakanin al’ummu daban daban, da tsakanin dan Adam da muhallin halittu.

Bisa tushen tunanin raya al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya ne, kasar Sin ta gabatar da karin shawarwari, irinsu Ziri Daya da Hanya Daya, da wadanda suka shafi kokarin tabbatar da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da cudanyar al’adu a duniya, ta yadda za a samu damar aiwatar da tunanin a harkokin dan Adam na fannoni daban daban.

Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya taba nanata cewa, yayin da ake aiwatar da tunanin raya al’ummar dan Adam, ba za a ce wasu al’adu sun fi wasu ba, kuma ba za a nemi maye gurbin wani tsarin al’umma da wani na daban ba. Maimakon haka, abin da za a yi shi ne hakuri da bambancin kasashe daban daban, ta fuskokin tsarin al’umma, da al’adu, da matsayin ci gaban tattalin arziki, sa’an nan a raba riba, da hakki, da nauyin aiki a tsakanin su, don tabbatar da makoma mai haske ta al’ummar dan Adam. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • Juventus ta sallami kocinta Thiago Motta
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  • Juventus za ta sallami kocinta Thiago Motta
  • Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
  • Hajiya Safara’u, Mahaifiyar Gwamna Raɗɗa Ta Rasu
  • Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu
  •  “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar