Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar NNPP ita ma ta shiga cikin rikici, inda ake zargin Kwankwaso ne ke jagorantar daya daga cikin bangarorin jam’iyyar.

A makon da ya gabata ne wani bangare na jam’iyyar NNPP karkashin jagorancin wanda ya assasa jam’iyyar, Dakta Boniface Aniebonam ya gudanar da babban taro a Legas, inda aka zabi sabbin mambobin kwamitin zartarwa na kasa.

Kwankwaso ya tabbatar da ganawarsa da Aregbesola a wani sako da ya fitar. Ya ce, “A yammacin yau na yi farin cikin ziyartar tsohon gwamnan Jihar Osun kuma tsohon ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, a gidansa da ke Legas. Taron ya ba mu damar tattaunawa a kan harkokin siyasar kasar nan da gudanar da mulki da kuma makomar dimokuradiyyar Nijeriya.”

Wata majiya mai tushe ta ce, “Taron ya ta’allaka ne kan yadda ‘yan siyasar biyu suka tsara dabarun makomarsu duba da irin matsalar da suke fuskanta a jam’iyyunsu. Don haka, zan iya cewa sun tattauna komai game da zaben 2027 ne.”

Wata majiya a bangaren Aregbesola ta bayyana cewa ‘yan siyasar biyu suna auna zabi hanyoyi daban-daban kafin 2027 kuma ana ci gaba da tattaunawa.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kwankwaso

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI

Shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Berry ya bayyana cewa HKI tanason jawosu cikin tattaunawar diblomasiyya wanda zai kai kasar ga samar da huldar jakadanci da ita, amma mu bama tare da wannan ra’ayin.

Nabih Berry ya bayyana haka ne a lokacinda yake zantawa da jaridar ‘Sharqul Awsad’ ya kuma kara da cewa a halin yanzu muja jiran HKI ta aiwatar da dukkan abubuwan da suka zo cikin yarjeniyar tsagaita wuta ta 1701 wacce kasashen duniya suka amince da ita, amma HKI ta ki aiwatar da ita a yayinda kungiyar Hizbullah ta luzumci tsagaita budewa juna wata na wannan yarjeniyar.

Shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya kara da cewa, a halin yanzu HKI take ficewa daga kasar Lebanon daga wasu wurare kimani biyar wanda hakan ya hana sojojin kasar Lebanon shiga wurare don tabbatar da cewa suna kula da dukkan kan iyakoki na kasar. Banda haka sojojin HKI suna keta hirumin wannan yarjeniyar, wanda yakata a aiwatar da ita watanni 6 da suka gabata. Tana kai hare-hare a kudancin kasar da kuma wasu wurare a Biqaa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]