Aminiya:
2025-04-14@20:40:09 GMT

Tinubu ya isa Ethiopia domin halartar taron AU

Published: 14th, February 2025 GMT

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya isa birnin Addis Ababa, na ƙasar Ethiopia domin halartar zaman taro karo na 38 na shugabannin ƙasashen ƙungiyar Afirka ta AU.

Shugaban wanda ya sauka a birnin Addis Ababa a daren ranar Alhamis ya samu tarba daga mataimakin shugaban kula da harkokin ƙasar Ethiopian, Eshetu Legesse da ministan harkokin waje, Ambasada Yusuf Tuggar da kuma mai kula da ofishin jakadancin Najeriya da ke Ethiopian, Ambasada Nasir Aminu.

Shugaban Ƙungiyar Afenifere, Adebanjo ya rasu Fursunoni 3 sun lashe Gasar Al-Ƙur’ani a Kano

Daga baya Ambasada Tuggar ya yi wa shugaba Tinubu bayani kan taron da kuma wasu nasarorin diflomasiyya da ƙasar ta samu, zaman da ya kai har misalin ƙarfe 2:00 na tsakar daren Juma’a.

Daga cikin nasarorin har da sake zaɓen Ambasada Bankole Adeoye a matsayin kwamishinan harkokin siyasa, zaman lafiya da tsaro na AU.

Har ila yau Najeriya ta ci gaba da zama a kwamitin zaman lafiya da tsaro na Ƙungiyar Afirka, yana mai jaddada, a cikin kalaman Ambasada Tuggar, “Jagorancin Najeriya da jajircewarta kan zaman lafiya da tsaro a nahiyar”.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana alhininsa akan rasuwar Dr. Akbar I’itimadi wanda shi ne na farko da ya kafa hukumar makamashin Nukiliya ta Iran.

Wasikar ta’aziyyar da shugaban kasa ta kunsa ta ambaci cewa:  Shakka babu hidima mai kima da wannan masanin ya yi, ya share fagen gina da ci gaban fasahar makamashin Nukiliya a Iran da kuma mayar da kasar mai cin gashin kanta a wannan fage.

Har ila yau, shugaban kasar ta Iran ya mika sakon ta’aziyyarsa ga masana na Iran, da kuma iyalansa. Ya kuma yi addu’a da rokon Allah madaukin sarki da ya lullube shi da rahamarsa da kuma gafararsa, sannan ya bai wa iyalansa na hakuri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • ‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Idris Ya Musanta Rahoton Wai Ya Ce A Yi Watsi Da Koken Gwamna Zulum Kan Rashin Tsaro A Borno