Aminiya:
2025-03-24@11:44:40 GMT

Tinubu ya isa Ethiopia domin halartar taron AU

Published: 14th, February 2025 GMT

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya isa birnin Addis Ababa, na ƙasar Ethiopia domin halartar zaman taro karo na 38 na shugabannin ƙasashen ƙungiyar Afirka ta AU.

Shugaban wanda ya sauka a birnin Addis Ababa a daren ranar Alhamis ya samu tarba daga mataimakin shugaban kula da harkokin ƙasar Ethiopian, Eshetu Legesse da ministan harkokin waje, Ambasada Yusuf Tuggar da kuma mai kula da ofishin jakadancin Najeriya da ke Ethiopian, Ambasada Nasir Aminu.

Shugaban Ƙungiyar Afenifere, Adebanjo ya rasu Fursunoni 3 sun lashe Gasar Al-Ƙur’ani a Kano

Daga baya Ambasada Tuggar ya yi wa shugaba Tinubu bayani kan taron da kuma wasu nasarorin diflomasiyya da ƙasar ta samu, zaman da ya kai har misalin ƙarfe 2:00 na tsakar daren Juma’a.

Daga cikin nasarorin har da sake zaɓen Ambasada Bankole Adeoye a matsayin kwamishinan harkokin siyasa, zaman lafiya da tsaro na AU.

Har ila yau Najeriya ta ci gaba da zama a kwamitin zaman lafiya da tsaro na Ƙungiyar Afirka, yana mai jaddada, a cikin kalaman Ambasada Tuggar, “Jagorancin Najeriya da jajircewarta kan zaman lafiya da tsaro a nahiyar”.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Sudan Sun Kwace Iko Da Fadar Shugaban Kasa A Birnin Khartum

Sojojin Sudan sun sanar a yau Juma’a cewa sun kwace iko da fadar shugaban kasa dake tsakiyar birnin Khartum, bayan da su ka kori mayakan rundunar kai daukin gaggawa.

Majiyar ta ce, sojojin na Sudan sun fara da kutsawa cikin fadar shugaban kasar ne, ta mashigar gabas,bayan da su ka kashe mayakan rundunar kai daukin gaggawa da dama,yayin da wasu da dama su ka gudu zuwa cikin kasuwar dake kusa.

Bayanin da sojojin na Sudan su ka fitar ya kunshi cewa; Mun murkushe mayakan Duqlu, ‘yan ta’adda a tsakiyar birnin Khartum da kuma kasuwar Larabawa da ginin fadar shugaban kasa da sauran ma’aikatu.”

Har ila yau majiyar sojan na Sudan ta ce,su kuma yi nasarar rusa makamai da motocin yakin rundunar kai daukin ggagawar,kamar kuma yadda ta kame wasu masu maya.

Janar Nabil Abdullah wanda shi ne kakakin sojan na Sudan ya sanar da cewa; Za su ci gaba kai hare-hare a cikin dukkanin fagagen yaki har samun nasara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • An Bude Taron Shekara-Shekara Na Dandalin Tattauna Raya Kasa Na Sin Na 2025
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Sojojin Sudan Sun Kwace Iko Da Fadar Shugaban Kasa A Birnin Khartum