Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Kammala Ziyararsa A Birtaniya
Published: 14th, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya kammala ziyarar da yake yi a Birtaniya.
Kakakin ma’aikatar Guo Jiakun ne ya bayyana hakan a yau, inda ya ce ziyarar ta Wang Yi ta cimma nasara da kyawawan sakamako. Ya ce wannan shi ne karon farko da ministan harkokin wajen Sin ya ziyarci Birtaniya cikin shekaru 10, kuma karon farko da Sin da Birtaniya suka gudanar da muhimmiyar tattaunawa cikin shekaru 7, lamarin dake nuna kudurin bangarorin biyu na ci gaba ingantawa da daidaita dangantakarsu.
Yayin taron, Sin da Birtaniya sun yi tattaunawa mai zurfi kan yanayin duniya da batutuwa masu daukar hankali da ma tsarin tafiyar da harkokin duniya, tare da cimma matsaya mai muhimmanci.
Bangarorin biyu sun bayyana niyyarsu ta tattaunawa cikin gaskiya bisa mutunta juna da kuma hakuri da bambance-bambancen da sabanin dake akwai a tsakaninsu. Har ila yau, sun amince cewa Sin da Birtaniya za su karfafa tuntubar juna da hada hannu wajen inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma ingiza ci gaban tattalin arzikin duniya. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka
Kasashen turan nan guda uku da ake wa lakabi da E3, sun nuna goyon bayansu ga tattaunawar da ake tsakanin Iran da Amurka.
Ministan Birtaniya mai kula da yammacin Asiya Hamish Falconer ne ya bayyana hakan inda ya ce Birtaniya tare da Faransa da Jamus na goyon bayan sasanta batun nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya.
A cikin sakon da ya wallafa, Falconer ya yaba da tattaunawar da akayi a babban birnin kasar Oman na Muscat a matsayin “muhimmiyar mataki na farko.”
Kuma a cewarsa “Birtaniya, tare da kawayenta na E3, a shirye suke don tallafawa tattaunawar.
A cikin 2018 a lokacin mulkinsa na farko, Trump ya janye Amurka daga yarjejeniyar da aka cimma a baya kan shirin nukiliyar Iran da kuma lafta mata tsauraren takunkumai amma kuma ya nuna aniyar kulla sabuwar yarjejeniya don maye gurbin waccen ta 2015.