Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin, Zhang Xiaogang ya fitar da sanarwa kan batutuwan da suka shafi aikin soja a baya-bayan nan. Ya ce, Taiwan wani bangare ne na kasar Sin. Kuma babu wata tsokana da sojojin Amurka za su yi da za ta iya canza wannan lamari, sabanin haka, za ta iya nuna munafuncin da Amurka ta dade ta na yi ga al’ummomin duniya, kuma za ta iya kara karfafa niyyar jama’ar kasar Sin ta kare ikon kasa da cimma cikakkiyar dunkulewar yankunan kasar baki daya.

Game da zarge-zarge marasa tushe da sabon ministan tsaron Amurka ya yi kan Sin, Zhang Xiaogang ya ce, Sin na adawa sosai da hakan. Kuma jama’ar kasar Sin na son zaman lafiya. Bugu da kari, ya ce a ko da yaushe, bangaren Sin ba zai tayar da yaki don habaka kasar ba, kuma ba zai yi watsi da iko da moriyarsa ba, kana zai tsaya tsayin daka kan tinkarar duk wata barazana da kalubale.(Safiyah Ma)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yemen: Amurka Ta Sake Kai Wani Harin A Kasar Yemen

Kasar Yemen ta sanar da cewa Amurka da ta sake kai wasu hare-haren a gundumar Hudaidah akan wani kamfani na auduga.

Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto majiyar Ansarullah ta  kasar Yemen din tana cewa; Sojojin na Yemen sun kai hare-hare da makamai masu linzami har 18 akan jiragen ruwa na dakon jiragen yaki “USS Troman” hari.

Kakakin sojan kasar Yemen ne janar Yahya Sari ya sanar da kai hare-hare na martani akan jiragen yakin Amurka.

Tun daga ranar Asabar din da ta gabata ne dai jiragen yakin Amurka da na Birtaniya su ka rika kai wa Yemen hare-hare da sun yi sanadiyyar shahadar mutane da dama.

Yankunan da harin ya shafa sun hada biranen San’aa da kuma Sa’adah, sai kuma Hudaidai.

A gefe daya shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik Husi, ya ce: hare-haren ta’adanci wadanda sojojin Amurka da Burtaniya suka kai kan yankuna da dama a kasar ba za su hana mutanen kasar ci gaba da kare Falasdinawa a Gaza ba.

Haka nan kuma ya kara da cewa:  Za  su ci gaba da kai hare hare a kan jiragen HKI da na Burtaniya da na Amurkan, masu wucewa ta tekun malia kamar yadda ta bayyana tun farko.

Kungiyar Ansarullah ta kasar yemen dai ta tallafawa Falasdinawa a yakin tufanul Aksa wanda aka fara a ranar 7 ga watan octoban shekara ta 2023, har zuwa lokacin da aka tsagaita wuta tsakanin Falasdinawa a Gaza da HKI a ranar 19 ga watan Jenerun shekara ta 2025.

Mayakan “Jubhatun-Nusrah’ Na Kasar Syria Sun Kai Hari Akan Iyakar Kasar Leabnon

A jiya Lahadi ne dai kungiyar ta ‘yan ta’adda ta kai hare-hare akan iyakar Lebanon  ta yankin Hermul

Ma’aikatar tsaron Syria ta fitar da wata sanarwa da a ciki ta riya cewa; harin nata martani akan wani hari da aka kai a can cikin kasar wanda ta jinginawa HIzbullah, da kuma ya yi sanadiyyar mutumar jami’an tsaro uku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya rantsar da Ibas a matsayin mai kula da Ribas
  •  Rasha Ta Sanar Da Kakkabo Da Jirage Marasa Matuki 57 Da Ukiraniya Ta Harba
  • Sojojin Kasar Yemen Sun Kai Wa HKI Hari Da Makami Mai Linzami
  • Yemen Ta Cilla Makamai Kan Kataparen Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Yaki Na Amurka A Tekun Red Sea
  • HKI Ta Nuna Damuwarta Da Jibge Sojojin Da Gwamnatin Masar Ta Yi A Yankin Sina
  • Wata 11 da tuɓe rawanin wasu sarakuna a Sakkwato
  • Atisayen Soji A Mashigin Tekun Taiwan Babban Gargadi Ne Ga ‘Yan Awaren Taiwan
  • Me Ya Sa Ba Za a Ba Yankin Taiwan Damar Samun ‘Yancin Kai Ba?
  • Yemen: Amurka Ta Sake Kai Wani Harin A Kasar Yemen
  • Iran Ta Yaba Da Yarjeniyar  Zaman Lafiya Da Aka Cimma Tsakanin Kasashen Armenia Da Azerbaijan