Aminiya:
2025-03-23@19:37:42 GMT

USAID na ɗaukar nauyin Boko Haram —Dan Majalisar Amurka

Published: 14th, February 2025 GMT

Dan Majalisar Dokokin Amurka, Scott Perry, ya yi ikirarin cewa Hukumar Raya Kasashe ta Amurka (USAID) ce ke ɗaukar nauyin kungiyoyin ta’addanci ciki har da Boko Haram.

Perry, dan jam’iyyar Republican mai wakiltar Pennsylvania, ya yi wannan ikirarin ne a taron sauraron sauraron ra’ayin na karamin kwamiti kan ingancin gwamnati a ranar Alhamis.

Kungiyar Boko Haram ta shafe sama da shekaru 15 tana kai hare-hare ayankin Arewa maso Gabashin Najeriya, inda ta kashe dubun-dubatar jama’a, ciki har da  ‘yan sanda, da sojoji da fararen hula.

Hare-haren kungiyar sun yi sanadin mutuwar yara fiye da 300,000, da raba mutun miliyan 2.3 da gidajensu da kuma haifar da matsalar abinci da yunwa a yankin.

A yayin zaman wanda ya mayar da hankali kan zargin karkatar da kudaden, Perry ya ce kuɗaɗen masu biyan haraji, “Dala miliyan 697 a duk shekara USAID krnkashewa, da kuma safarar kudaden kudade kungiyoyin ISIS da Al-Qaeda da Boko Haram da ISIS Khorasan, da kuma sansanonin horar da ’yan ta’adda.”

Ya kuma ce hukumar ta USAID ta bayar da dala miliyan 136 don gina makarantu 120 a Pakistan, inda ya yi zargin wata shaida ko da ke nuna gina makarantun.

Shugaba Donald Trump ya bayar da umarnin rufe hukumar ta USAID, kan zargin ta da cin hanci da rashawa a wani sako da ya wallafa.

Shi ma Elon Musk, abokin Trump, kuma shugaban ma’aikatar kula da ayyukan gwamnati, ya soki hukumar ta USAID, yana mai zargin cewa tana gudanar da ayyukan damfara.

Daga cikin wasu sukar, Musk ya yi iƙirarin cewa USAID tana “aikin leƙen asiri kamar CIA” har ma da “binciken kuɗaɗen binciken makaman ƙare-dangi, gami da COVID-19, wanda ya kashe miliyoyin mutane.”

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Ibnu Juzai al-Kalbi Allah Ya yi masa ranama yan nuna mana munin hassada ta fuska biyu:

1. A Ɗabi’a: Hassada tana haifar da cutar zuciya, wadda ke hana mutum farin ciki da jin daɗin rayuwa, kuma tana sa mai yin ta ya zama mai mugun hali, da ƙoƙarin ganin wani ya faɗi ko ya rasa abin da ya samu. A al’ada, mutane suna ƙin mai hassada saboda halayensa na rashin son alheri ga mutane da kuma fatan sharri a gare su.

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

2. A Shari’a: A cikin Alƙur’ani, Allah ya yi umurni da a nemi tsari a wurinsa daga hassadar mahassadi, inda Ya ce:” Ka ce:” Ina neman tsari da Ubangijin asuba. Daga sharrin abin da Ya halitta. Da kuma sharrin dare idan ya lulluɓe da duhu. Da kuma sharrin mata masu tofi a cikin ƙulle-ƙulle. Da kumma sharrin mahassadi yayin da ya yi hassada.” Suratul Falaƙ aya ta 1-5. Manzon Allah (ﷺ) ya ce: “Kada ku yi hassada da juna…” Muslim ne ya ruwaito [#2563].

Hassada tana iya kai mutum ga saɓawa Allah, kamar yadda Shaiɗan ya ƙi yin sujada ga Adam saboda kishi da hassada. Hassada tana haifar da cin amanar ‘yan’uwa, da munafunci, da karya. Hassada tana cutar da mai yin ta fiye da wanda ake yi wa. A ɗabi’a, tana hana kwanciyar hankali, a shari’a kuwa tana kai mutum ga zunubi. Maimakon yin hassada, Musulumi ya kamata ya roƙi Allah ya ba shi alheri kamar yadda Ya ba wa waninsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • MDD da EU sun yi tir da wargaza yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da Isra’ila ta yi
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Jagora: Amurka Ta Kwana Da Sanin Cewa Ba  Wata Riba Da Za Ta Ci Ta Hanyar Yi Wa  Iran Barazana
  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]