Leadership News Hausa:
2025-04-15@23:27:06 GMT

GORON JUMA’A 14-02-2025

Published: 14th, February 2025 GMT

GORON JUMA’A 14-02-2025

Da farko ina yi wa daukacin al’unar musulmi barka da juna’a, sannan ina gaishe da mahaifiyata Haj. Asma’u da kuma mahaifina Alh. Yusif Gwani, ina gaida kawayena kamar su; Maryam, islam, da sauran kawayena na islamiyya.

Sako daga Fatima Yahaya Jihar Bauchi:

Ina mika sakon juma’a ta ga masoyina abun alfaharina uban ‘ya’yana kn sha Allah Al’amin, ina gaishe da kannen masoyina Ali, Ibrahim, Amina, Hamid, Fa’iza, ina fatan za su yi juma’a lafiya.

Sako daga Khalil Isah Muhammad Jihar Kano:

Ina gaishe da iyayena da abokaina kamar su; Ahmad dan gajere, Musbahu karkasara, Tahir, da kuma Zulyadaini Salis.

Sako daga Aisha Muhammad Birnin Kudu:

Dan Allah ina so a mika mun sakon gaisuwa ta zuwa ga Samira Muktar, da kuma Iklima Auwal da Jabir Usman, Ummy zee, da Kabir T.Y, fatan za su yi juma’a lafiya.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda

’Yan sanda sun kama shahararren mawaƙin zamani a Najeriya Habeeb Okikiola Badmus, wanda aka fi sani da Portable, bayan ƙazancewar rikicinsa da fitaccen ƙwararren mawakin Fuji, Okunola Saheed “Osupa.”

A ranar Lahadi da dare ne ’yan sanda daga Jihar Kwara suka yi takakkiya suka kamo Portable mai waƙar “Zazu Zeh” a garin Abeokuta, Jihar Ogun

Kakakin ’yan sanda na Jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ya ce an kama Portable bayan samun takardar ƙorafin da Osupa ya aike ɗauke da jerin manyan zarge-zarge da yake yi wa mawakin na “Zazu Zeh,” na ɓata suna, barazanar kisa, tunzura jama’a, zubar da da mutum da gangan, neman tayar da fitina, da kuma amfani da zagi da munanan kalamai.

“Saboda girman waɗannan zarge-zarge da kuma ingantattun shaidun da aka gabatar, rundunar ta samu sammacin kame daga Kotun Majiatare da ke zamanta a Ilorin, inda jami’anmu suka je Abeokuta, suka kamo wanda ake zargin suka kawo shi Ilorin domin ci gaba da bincike.”

Jami’in ya ce da kawo Portable jihar Kwara, nan take aka fara yi masa Portable tambayoyi da ɗaukar bayanansa a gaban lauyoyi daga bangarorin biyu.

Ya tabbatar da cewa Portable zai ci gaba da kasancewa a tsare kuma nan ba da komawa ba za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Rigimar mai zafi, tsakanin Portable da Osupa, ta samo asali ne daga rashin jituwa kan keta haƙƙin mallakar waƙa. Wannan rashin jituwa ta ɓarke ne a bainar jama’a lokacin da Portable ya yi amfani da zagi ga fitaccen mawakin na Fuji mai shekaru 55 a wani bidiyo da ya yaɗu, wanda ya jawo caccaka a kafafen sada zumunta.

A cikin bidiyo, Portable ya bayyana cewa, “Kuɗi ne ya jawo faɗan!” yana ƙoƙarin bayyana ɓacin ransa. Ya ce “Raina ya ɓaci ne saboda ina so a ba ni kuɗina, kuma na ji suna ƙoƙarin sauke waƙar.”

Bayan shan caccaka daga bisani ya saki wani bidiyo yana neman afuwar Osupa cikin girmamawa. Ya ce, “Sarki Saheed Osupa, babana, don Allah kada ka yi fushi. Ka ɗauke ni kamar ɗanka ka horar da ni.”

A wani yanayi mai ban mamaki kuma, Portable ya nuna cewa rigimar tasu wani salon neman magoya baya ne, har ma ya nemi a ba shi damar gudanar da wasanni. “Dukkanmu muna tallata kanmu… don Allah a ba ni aiki.”

Sai dai, Saheed Osupa ya yi watsi da neman afuwar a matsayin wanda bai isa ba, yana mai cewa dole Portable ya samu sakamakon abin da ya aikata.

Ƙi amincewar tasa ba ta yi wa Portable daɗi ba, har ya ƙi janyewa, inda a ƙarshe ya kai ga matakin da Osupa ya ɗauka na shigar da ƙara ga hukumar ’yan sanda.

Yanzu, duniyar nishaɗi ta zura ido tana kallon yadda za a ƙare a wannan rikici  manyan mawaka da ya tashi daga kafafen sada zumunta zuwa zauren kotu.

Shin Portable zai fuskanci cikakken hukuncin doka bisa ga zarge-zargen da ake yi masa, ko kuwa za a samu sasanci ne?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 109
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari