HausaTv:
2025-03-23@03:23:48 GMT

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Hadu Da Fushin ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa

Published: 14th, February 2025 GMT

‘Yan gwagwarmayar Falasdinawa suna ci gaba da mayar da martini kan hare-haren wuce gona da iri da sojojin mamayar Isra’ila suke kai wa kan gabar yammacin kogin Jordan

Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da kai farmakin soji a cikin dare da safiyar kan garuruwan da suke gabar yammacin kogin Jordan, inda sojojin mamayar suka kaddamar da munanan hare-hare a kan sansanin Jenin sannan wani jirgin yakin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi luguden bama-bamai kan gidajen Falasdinawa.

A gefe guda kuma, ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa sun gudanar da arangamar da sojojin mamayar, a sansanin Askar da ke gabashin Nablus. Yayin da a birnin Nablus aka yi artabu mai tsanani tsakanin ‘yan gwagwarmayar na Falasdinu da sojojin mamayar Isra’ila.

A halin da ake ciki kuma, Bataliyar Nablus da ke karkashin Sarayal-Quds na kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da kai wa sojojin mamayar Isra’ila hari da harsasai da tada bama-bamai, yayin da dakarun shahidan Al-Aqsa suka tabbatar da gwabza kazamin fada da sojojin mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin mamayar Isra ila da sojojin mamayar

এছাড়াও পড়ুন:

A cikin kwanaki 3 Falasdinawa 605 sun yi shahada a kisan kiyashin Isra’ila a Gaza

Daruruwan Falastinawa fararen hula ne suka yi shahada tun bayan da Isra’ila ta dawo da hare-haren kisan kare dangi a kan al’ummar yankin zirin gaza, matakin day a yi hannun riga baki daya da yarejejeniyar dakatar da bude wuta da aka rattaba hannu a kanta karkashin jagorancin Amurka, Masar da kuma Qatar.

Dakarun mamaya na Isra’ila sun kaddamar da wani farmaki mai matukar muni da manyan makamai a ranar Juma’a a kan yankunan arewa maso yammacin Gaza da suka hada da Sudaniya, al-Karamah, da kuma Beit Lahia, wanda hakan ya yi sanadin shahadar fararen hula masu yawa da suka hada da mata da kananan yara, yayin da kuma wasu daruruwa suka jikkata.

Sojojin Isra’ila sun yi gargadi ga dukkanin Falasdinawa mazauna yankunan  Sultan, Karama, da Awda da ke arewacin zirin Gaza, inda suka bukace su da su bar gidajensu, su koma zuwa yankunan kudancin Gaza.

Majiyoyin cikin gida sun ba da rahoton cewa, an kai wasu wadanda suka samu raunuka da dama da suka hada da wanda ke cikin mawuyacin hali zuwa asibitin Indonesiya da ke arewacin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa
  • Falasdinawa 80,000 ne suka halarci sallar Juma’a a mako na uku na Ramadan a masallacin Al-Aqsa
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • A cikin kwanaki 3 Falasdinawa 605 sun yi shahada a kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Yaffa Kusa Da Tel Aviv A Karo Na Biyu A Cikin Sa’o’i 24
  • Sojojin HKI Sun Kara Kisan Karin Falasdinawa 71 A Zirin Gaza
  • Sojojin Yamen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • Hare-Haren Isra’ila Cikin Dare Sun Hallaka Mutum Aƙalla 50 A Gaza