Masana’antar Samar Da Injuna Ta Kasar Sin Ta Samu Tagomashi A 2024
Published: 14th, February 2025 GMT
Kungiyar masu sana’ar samar da manyan injuna ta kasar Sin ta bayyana a yau Juma’a cewa, masana’antar ta samu ci gaba mai inganci a shekarar 2024, biyo bayan shirin kasar na daukaka ingancin manyan injuna da ma dabarun raya masana’antar da aka dauka.
A shekarar 2024, ribar da manyan kamfanonin samar da manyan injuna suka samu ya karu kan na 2023 da kaso 6 cikin dari.
A bara, na’urorin samar da lantarki daga iska ne suka mamaye fiye da rabin kayayyakin samar da lantarki a kasar.
A shekarar 2024, cinikin motoci masu amfani da makamashi mai tsafta ne ya dauki kaso 40.9 na jimilar cinikin motoci a kasar. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ba Zata Yarda A Kafa Kasar Palasdinu Ba, Saboda Barazana Ce Ga Wanzuwar HKI
Ministan tsaron HKI Israel Katz ya bayyana cewa gwamnatin HKIba zata bar a kafa kasar Falasdinu ba, saboda hakan barazana ce ga samuwar HKI.
Israek Kazt ya bayyana haka ne a lokacin ganawar jami’an gwamnatin HKI da tawagar kasar Amurka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a taron su da tawagar kasar ta Amurka a yau. Ya kuma kara da cewa abubuwan da HKI ta sa a gaba sun hada da ganin kasar Iran bata mallaki makaman Nukliya ba, da shafe kungiyar hamas, sakin fursinoni a hannun Hamasa da kuma samar da huldar jakadanci da kasar Saudiya.
Wasu kafafen yada labarai sun nakalto wasu manya manyan jami’an sojojin kasar suna tunanin dakatar da tsagaita wuta da suka kulla da Hamas. Banda haka suna ganin shawarar shugaba kasar Amurka Donal Trump n araba gaza da Falasdinawa ne kawai zai tabbatar da wanzuwar HKI.
Kafin haka dai Banyamin Natanyahu ya fadawa kafafen yada labarai kan cewa Falasdinawa suna da damar su bar Gaza su je inda suka ga dama, idan sun bukaci hakan, amma idan bas u yi ba, to mai yuwa a kashesu gaba daya.