Jakadan Iran a Lebanon ya bayyana cewa: Suna maraba da matakin jigilar jiragen saman Lebanon zuwa Iran da sharadin rashin soke jigilar jiragen Iran zuwa Lebanon

Jakadan kasar Iran a kasar Lebanon Mujtaba Amani ya bayyana cewa: Bangaren Iran yana maraba da samar da jigilar jiragen saman kamfanonin jiragen saman kasar Lebanon zuwa kasar Iran, ba tare da batun soke jigilar jiragen saman Iran zuwa kasar Lebanon ba.

Gidan talabijin din kasar Iran a yau Juma’a ya sanar da cewa: An yi watsi da furucin wasu kamfanonin jiragen sama guda biyu da suka ce, gwamnatin Lebanon ta hana tafiyar jiragen saman Iran guda biyu zuwa kasar Lebanon da suke tashi a ranakun Alhamis da Juma’a, don haka ofishin jakadancin Iran a Lebanon ya bi sawun abin da ke faruwa, inda aka gyara matsalar ta hanyar tabbatar da izinin ci gaba da jigilar jiragen, tare da sanar da matafiya daga Iran zuwa Lebanon gudanar da tafiye-tafiyensu daga Iran zuwa Lebanon.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kasar Lebanon jigilar jiragen jiragen saman

এছাড়াও পড়ুন:

 Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen

Rahotanni daga kasar Yemen sun ambaci cewa jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-hare a yankuna mabanbanta na kasar Yemen da su ka hada da birnin San’aa.

Tashar talabijin din al-masirah ta ambaci cewa; jiragen yakin Amurka sun kai hare-haran ne har sau 7, biyu a cikin yankin Hamadan, da Banu Hashish sai kuma babban birnin kasar Sanaa.

Kawo ya zuwa babu cikakken bayani akan adadin wadanda su ka jikkata ko shahada sanadiyyar wannan harin.

Amurkan dai tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda taimakawa HKI a yaki, da kokarin hana dakarun Ansarullah ci gaba da kai hare-hare akan manufofin HKI.

A daren jiya Alhamsi shugaban kungiyar Ansarullah Sayyid Abdulmalik al-Husi ya  bayyana cewa; hare-haren da Amurka take kai musu ba su yi wa makaman da suke da su illa ba,kuma akasin haka suna kara musu azama ne.

Sojojin Yemen suna kai hare-hare a HKI saboda yin matsin lamba akan HKI ta dakatar da hare-haren da take kai wa Gaza, sannan kuma da mayar da martani akan jiragen dakon jiragen yaki na Amurka a tekun “Red Sea’ bayan da su ka fara kai wa Yemen din hari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Amnesty Ta Zargi  Rundunar “RSF” Ta Sudan Da Cin Zarafin Mata
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)
  • Sin Za Ta Kara Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar Zuwa 125%
  • GORON JUMA’A
  • Hizbullah ta kirayi gwamnatin Lebanon da ta dauki mataki kan hare-haren Isra’ila
  •  Amurka Ta Kai Hare-hare A Yankunan Kasa Yemen
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu