Aminiya:
2025-04-14@20:12:10 GMT

Asabar ne zaɓen ƙananan hukumomin Jihar Katsina 

Published: 14th, February 2025 GMT

Kamar yadda doka ta tanada cewar duk wata ƙaramar hukumar a tabbatar da cewa zaɓaɓɓun shugabanni ne ke jagorancin ta.

Wannan ya sa Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Umar Dikko Raɗɗa ta shirya aiwatar da zaɓen ƙananan hukumomi 34 da ke faɗin jahar wanda hakan zai ƙara ba su damar cin gashin kan su kamar yadda dokar ƙasa ta tanadar.

Mutum 23 sun mutu da raunata wasu a haɗarin mota a gadar Kano Shugaban Ƙungiyar Afenifere, Adebanjo ya rasu

Kamar yadda shugaban Hukumar zaɓen mai zaman kanta ta Jihar Alhaji Lawal Alhassan Faskari ya shaidawa manema labarai a lokacin da ake rarraba kayan zaɓen zuwa ƙananan hukumomin jihar ya ce, tuni hukumar zaɓen ta kammala duk wasu shirye-shirye don ganin anyi zaɓen bisa doka.

Hakan ya sa aka ba kowace jam’iya damar fito da wanda zai yi mata takarar kujerar ƙaramar hukumar ko ta Kansila. Sai dai abin da mafi yawan jama’a suka yi tsammani cewar babbar jam’iyar adawa ta PDP ba za ta shiga zaɓen ba bisa dalilanta na cewa, ba sahihin zaɓe ne za a yi ba.

Duk da hakan bai hana wasu jam’iyun shiga cikin wannan zaɓe ba. Jam’iyar Accord da Booth da AAC da ADC sun shiga cikin wannan zaɓe.

Dangane da wuraren da ake fama da matsalar tsaro kuwa, an shirya gudanar da yin zaɓukan su a wasu wurare da aka tanada a yankunansu kamar yadda aka yi a zaɓukan da suka gabata.

Duk da haka kuma hukumomin tsaro a jihar sun ja hankali tare da gargaɗi ga masu ƙoƙarin kawo wata fitina da gargaɗin su ko su fuskanci fushin hukuma.

Kazalika, an hana zirga zirgar ababen hawa in baya ga na musamman da kuma masu gudanar da aiyukan zaɓen.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume

Sanatan Kudancin Borno, Ali Ndume, ya bayyana cewa a halin yanzu mayaƙan Boko Haram sun ƙwace yankunan ƙananan hukumomi uku a jihar.

Ndume ya bayyana cewa mayaƙan kungiyar sun kashe fararen hula sanda a 200 da sojoji 100 a sabbin hare-haren da suka kai a sassan jihar a baya-bayan nan.

A wata zantawar da aya yi da ’yan jarida a ƙarshen mako, ɗan Majalisar Dattawan ya ce mayaƙan Boko Haram sun kai hare-hare 252 a daga watan Nuwamban 2024 zuwa yanzu.

Ya bayyana damuwa game da dawowar munanan ayyukan kungiyar a jihar duk kuwa da kokarin da sojoji da sauran hukumomin tsaro ke yi domin murƙushe su.

Abincin karnuka ya fi wanda ake ba mu —Fursunonin Najeriya NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno

A sakamako haka ne ya ce sanatoci da ’yan majalisar wakilan Jihar Borno da Gwamna Babagana Zukum, suka yi zama da sojoji da sauran hukumomin tsaro domin shawo kan matsalar.

Da yake tsokaci kan dawowar hare-haren, Sanata Ndume ya ce, “Wannan abin damuwa ne, duk da cewa sojoji sun halaka ’yan ta’adda sama da 800, su kuma ’yan ta’addan su kashe sama da 500 a sakamakon rikicin ISWAP da Boko Haram.”

Ya ce, “daga watan Nuwambar 2024 zuwa yanzu sun kai hare-hare 252, sun kashe sojoji 100 da fararen hula 500. Yanzu haka kuma kananan hukumomi uku na Jihar Borno — Gudumbari, Maye da Abadam — na hannunsu,” haka zalika sun tarwatsa wasu sansanonin soji da ke wurin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu
  • Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)