Kasar Iran ta bayyana cewa: Barazanar gwamnatin mamayar Isra’ila ga jirgin saman da ke dauke da fararen hula na Lebanon cin zarafi ne ga ‘yancin kasar Lebanon

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi Allah wadai tare da tofin Allah tsine kan barazanar da gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta yi wa jirgin farar hula da ke dauke da ‘yan kasar Lebanon, yana mai nuni da hakan a matsayin ci gaba da keta ka’idoji da dokokin kasa da kasa a fili, da kuma keta hurumin kasar Lebanon.

Baqa’i ya yi nuni da cewa: Barazanar da gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta yi wa jirgin farar hula da ke dauke da ‘yan kasar Lebanon, wanda hakan ya haifar da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama na fararen hula na yau da kullun zuwa filin jirgin saman birnin Beirut, yana mai cewa: Wannan mataki da gwamnatin mamayar Isra’ila ta dauka ci gaba ne da keta ka’idoji da dokokin kasa da kasa a fili, da kuma keta hurumin kasar Lebanon.

Ya kuma yi kira da a dauki tsauraran matakai daga kungiyoyin kasa da kasa da abin ya shafa, ciki har da hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta kasa da kasa (ICAO), domin dakile munanan dabi’un da haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan aminci da tsaron jiragen sama.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiyan, a sakonsa na karshe ga Iraniyawa a shekara ta 1403 na kalandar Iraniyawa, ya bukaci mutanen kasar su hada kai don kaiwa ga manufofin kasar, wadanda suka hada da bunkasar tattalin arziki, da kauda tsadar rayuwa da kuma rashin bawa makiya damar cutar da kasar.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jawabinda na ‘Nuruz’ ko sabon shekara ta 1404 wanda ya shigo yau. Pezeshkiyan ya bukaci All…ya yi rahama ga shuwagabannimmu da muka rasa a shekaran da ta kare, wadanda suka hada da Shahid Ibrahim Ra’isi da abokan tafiyar, da sharing maso gwagwarmaya a ciki da wajen kasar, wadanda suka hada da shahidan Lebanon Falasdin Siriya da sauransu. Sannan yayi fatan sabuwar shekara ta 1404 mai albarka ga mutanen kasar da kuma sauran masoya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gudanar da gagarumar zanga-zangar nuna goyon bayan Falastinu a kasar Jordan
  • Saree: Filin jirgin saman Ben Gurion ba shi da aminci har sai an kawo karshen yakin Isra’ila a Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • Jiragen Yakin HKI Sun Kai Hare-Haren Kan Wasu Wurare A Gabaci Da Kuma Kudancin Kasar Lebanon
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
  • Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas
  • OIC ta yi Allah wadai da sake dawo da hare-haren yahudawan sahyuniya a kan a zirin Gaza
  • Sojojin Yamen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya
  • Jami’i: Jiragen Saman Kasar Sin Za Su Bunkasa Sashen Sufurin Jiragen Afirka