An ɗage taron mahaddata Qur’ani da za a yi a Abuja
Published: 14th, February 2025 GMT
Rahotanni sun nuna cewa an ɗage taron mahaddata al-Qur’ani da ake yi wa laƙabi da Qur’anic Convention a Turance da ya rage ƙasa da mako biyu wanda za a gudanar a Abuja kamar yadda BBC Hausa ta bayyana.
An dai ranar Asabar 22 ga watan Fabrairu na 2025 a matsayin ranar da za a gudanar da taron da ake sa ran zai samu mahalarta waɗanda mahaddata Qur’ani ne sama da dubu 60 daga ciki da wajen Najeriya.
Wani ɗan kwamitin tsara taron wanda bai so a ambaci sunansa ba ya shaida wa BBC cewa, “tun daren jiya Alhamis aka ɗage yin wannan taro.
Sai dai kuma majiyar ba ta tabbatar wa da BBC dalilin da ya sa aka ɗage taron ba da kuma yaushe ne sabon lokacin da za a yi taron a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan ta’adda Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Uku A Borno
Hakan ya sa, rundunar FOB ta yi kira da akawo musu dauki ta sama baya ga aikewa da karin tawaga ta kasa domin tallafawa. Duk da haka, tawagar ta sake cin karo da Bam a kan hanya.
Duk da cewa, ba a samu cikakken bayanin harin ba a lokacin rubuta wannan rahoton, amma an samu cewa, matukin jirgin yakin da aka aika domin bayar da agaji ta sama, ya sanar da cewa, yana iya hango wuta tana ta shi a kusa da FOB sannan wasu sojoji da dama na gudu zuwa Sabon Gari, kamar dai, an riga an kwace sansanin FOB din.”
Darakta, Ayyukan Yada Labarai na Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, bai amsa sakon da Wakilinmu ya aika masa ba domin tabbatarwa a lokacin fitar da wannan rahoton.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp