Aminiya:
2025-02-20@08:58:59 GMT

Bidiyon TikTok: Jami’ar UNIZIK ta kori ɗalibar da ta ci kwalar malami

Published: 14th, February 2025 GMT

Hukumomin Jami’ar Nnamdi Azikiwe (Unizik) da ke, Awka a Jihar Anambra ta kori ɗalibar nan mai suna Goddy-Mbakwe Chimamaka Precious, saboda cin kwalar wani malamin jami’ar Dakta Chukwudi Okoye.

A cikin wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta an ga Goddy-Mbakwe ta far wa malamin jami’ar, Dakta Chukwudi bayan ya ratsa ta cikin bidiyon da take ɗauka a wani wuri da ke harabar jami’ar.

An ɗage taron mahaddata Qur’ani da za a yi a Abuja Asabar za a yi zaɓen ƙananan hukumomin Katsina

A cikin takardar korar ɗalibar da jami’ar ta fitar mai ɗauke da kwanan watan 13 ga watan Fabrairu, wanda muƙaddashin magatakardar jami’ar, Ɓictor I. Modebelu ya sanya wa hannu, ta ce an ɗauki matakin korar ne bayan shawarar kwamitin bincike da jami’ar ta yi.

Hukumar jami’ar ta ce ”Kwamitin ya samu ɗalibar da laifin saɓa wa dokokin ladabtarwa na jami’ar, musamman sashe na 4 na dokar ladabtarwa ta (SDR)”, in ji takardar korar.

Bidiyon cin kwalar malamin ya ja hankalin mutane da dama a shafukan sada zumunta, inda aka yi ta kiraye-kirayen ɗaukar mataki kan lamarin.

Hukumar Jami’ar ta buƙaci ɗalibar da ta gaggauta ficewa daga harabar jami’ar tare da mayar wa jami’ar duk wasu abubuwan da ke hannun ɗalibar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗalibar da

এছাড়াও পড়ুন:

Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa: Barazanar Makiya Kan Iran Ba Zata Yi Nasara Ba

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Barazanar makiya a kan kasar Iran da al’ummarta ba ta yi nasara ba

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa: Gagarumar zanga-zamga da al’ummar Iran suka gudanar a ranar 22 ga watan Bahman ta tabbatar da cewa barazanar makiya a kan Iran da al’ummarta ba ta cimma nasara ko yin tasiri ba.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin yayin da yake karbar bakwancin dubban mutane daga lardin gabashin Azarbaijan a Husainiyar Imam Khumaini da ke Tehran fadar mulkin kasar a ranar Litinin din da ta gabata, a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan zagayowar bore mai tarihi na al’ummar Tabriz a ranar 29 ga watan Bahman shekara ta 1356 wanda ya zo daidai da (18 ga watan Fabrairu shekara ta 1978), ya bayyana cewa: Tsare-tsaren barazana ta hanyar wasa da ra’ayin al’umma da watsa sabani kan neman haifar da shakku dangane da kotunan juyin juya halin Musulunci da kuma yada kokwanto game da iya kalubalantar makiya.

Jagoran ya kara da cewa: A wannan taro da ya samu halartar shugaban kasar Masoud Pezeshkian suna jaddada cewa: Makiya suna kokarin tarwatsa al’umma ta hanyar yaudara amma da yardan Allah har yanzu ba su samu nasara ba, kamar yadda suke kokarin girgiza zukatan al’ummar Iran da neman hana matasa samun karfin gwiwar himma da hubbasa a fagen kara ci gaban kasarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ASUU Reshen Jami’ar KASU Ta Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Bayyana Cewa: Barazanar Makiya Kan Iran Ba Zata Yi Nasara Ba
  • Jaridar Maariv Ta Isra’ila Ta Bayyana Wasu Daga Cikin Hasarorin Da Yakin Gaza Ya Janyo Wa Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • Da Dama Sun Rasu Yayin Da NAF Ta Kai Wa ‘Yan Bindiga Hari A Katsina
  • Kasar Sin Ta Taya Mahmoud Ali Youssouf Murnar Zabarsa Da Aka Yi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar AU
  • Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon
  • Hukumar Kula Da Ayyukan Duba-gari Ta Kasa Za Ta Karrama Shugaba Tinubu 
  • Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau