Aminiya:
2025-02-20@09:10:34 GMT

Gobara ta ƙone ofishin zaɓe INEC a Sakkwato

Published: 14th, February 2025 GMT

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce ofishinta na Ƙaramar hukumar Gwadabawa da ke Jihar Sakkwato ya ƙone ƙurmus, inda  gobarar ta lalata akwatunan zaɓe da sauran kayayyaki.

Mista Sam Olumekun, kwamishinan Hukumar INEC kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a wata sanarwa.

Mutum 23 sun mutu da raunata wasu a haɗarin mota a gadar Kano Tinubu ya isa Ethiopia domin halartar taron AU

A cewarsa, a taron Hukumar INEC na mako-mako da aka saba gudanarwa a ranar Alhamis, hukumar ta lura da wani mummunan lamari na tashin gobara a ofishin ƙaramar hukumar Gwadabawa da ke Jihar Sakkwato, kamar yadda sakatariyar gudanarwa mai kula da ofishin jihar, Hauwa Aliyu Kangiwa ta ruwaito.

Ya ce gobarar ta tashi ne da sanyin safiyar Talata 11 ga watan Fabrairun 2025.

“Duk ginin ofishin ya lalace. Kayayyakin da suka lalace sun haɗa da tebura da kujeru da kayan aiki da kayan zaɓe da ake iya ɗauka, daga cikinsu akwai akwatunan zaɓe 558, rumfar kaɗa ƙuri’a 186, jakunkuna 186 na zaɓe da kuma kayayyakin da suka haɗa da manyan tankunan ruwa guda 12 (litta 1,000), tabarmin barci 400 da bokitan robobi 300.

“Rahoto na farko daga ofishinmu na jihar ya nuna cewa an samu ƙaruwar wutar lantarki kafin faruwar lamarin,” in ji Olumekun.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwadabawa Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi

Majalisar Wakilai ta umarci kwamitinta kan harkokin zaɓe da ya binciki Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC dangane da jinkirin da take yi na gudanar da zaɓen cike giɓin wasu kujerun ’yan majalisar tarayya da na jihohi.

Majalisar a wannan Talatar ta kuma bayyana cewa jazaman ne kwamitin ya gayyaci Hukumar INEC domin ta bayar da dalilai kan tsaikon da aka samu da kuma yadda take ƙoƙarin yi wa tufkar hanci.

Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara Da wahala City ta yi nasara a gidan Madrid — Guardiola

Aminiya ta ruwaito cewa Majalisar ta buƙaci kwamitin ya sauke wannan nauyi tare da miƙa mata rahoton bincikensa nan da makonni huɗu.

Wannan dai na zuwa ne bayan ƙorafin da wani ɗan majalisar, Jafaru Leko ya gabatar yana mai kafa hujja da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya wanda ya ɗora wa INEC alhakin gudanar da zaɓe a faɗin ƙasar.

Kazalika, ya naƙalto sassa na 47 da 90 da ke cikin Kundin Tsarin Mulkin wanda ya hukunta assasa majalisun tarayya da na jihohi a matsayin wani rukuni na ’yancin ’yan ƙasa su samu wakilci.

Ya yi ƙorafin cewa tun bayan Zaɓen 2023 da waɗanda suka biyo baya, an samu giɓi a majalisun tarayya da na jihohi saboda wasu dalilai kamar mutuwa, karɓar wasu muƙaman ko ajiye aiki.

Jafara Leko ya ci gaba da ƙorafin cewa Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya yi tanadin gudanar da zaɓen cike giɓi cikin tsawon lokacin da bai gaza wata guda ba da samun giɓin.

Ya ƙara da cewa, gudanar da zaɓen wanda alhakinsa ya rataya a wuyan Hukumar INEC shi ne zai tabbatar da wakilcin kowace mazaɓa a ƙasar.

A cewarsa, wannan jinkiri da INEC take ci gaba da yi rashin biyayya ne ga Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, lamarin da ke cutar da al’umma ko mazaɓar da ba su wakilci a hukumance.

Aminiya ta ruwaito cewa, a halin yanzu akwai kujerun ’yan Majalisar Tarayya bakwai masu giɓi da suka haɗa da na Majalisar Wakilai biyar da kuma biyu a Majalisar Dattawa.

Kujerun da ke da giɓi a Majalisar Wakilan sun haɗa da na jihohin Edo, Oyo, Kaduna, Ogun da Jigawa sai kuma na Majalisar Dattawa da suka ƙunshi Edo da Anambra.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’in tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato
  • Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi
  • Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi
  • Hajji 2025: Kamfanin Saudiyya zai maka Najeriya a Kotun Duniya
  • Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
  • Gobara ta yi ajalin uwa da ’ya’yanta a Ondo
  • Kasar Sin Ta Taya Mahmoud Ali Youssouf Murnar Zabarsa Da Aka Yi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar AU
  • Hukumar Kula Da Ayyukan Duba-gari Ta Kasa Za Ta Karrama Shugaba Tinubu