HausaTv:
2025-03-22@12:54:46 GMT

Iran Ta Sanar Da Samun Sakwanni Daga Mahukuntan Syria

Published: 15th, February 2025 GMT

Babban jami’i mai kula da harkokin Syria a ma’aikatar harkokin wajen Iran, Muhammad Ridha Ra’uf Shaibani ya sanar da cewa, sun  yi musayar  sakwanni da kasar Syria, kuma sun bude kafar ttataunawa ta kai tsaye.

Ra’uf Shaibani wanda ya kai ziyara kasar Rasha domin ttataunawa da mahukuntan kasar, ya fada a jiya Juma’a da marece cewa, Muna cikin shiri da tanadin sake dawo da alaka da kasar Syria anan gaba.

Har ila yau. Shaibani ya ce; Muna bin diddigin abubuwan da suke faruwa a Syria, kuma za mu dauki matsaya a lokacin da ya dace.”

Haka nan kuma ya ce; Muna kallon Syria ne a matsayin kasa wacce take da matsayi a cikin yankin yammacin Asiya, kuma mun yi imani da cewa, al’ummar kasar ne za su ayyana makomarta, don haka ya zama wajibi dukkanin bangarorin siyasar da ake da su a kasar su shiga ayi da su.”

Dangane da ziyarar da ya kai kasar Rasha, Shaibani ya ce; yana yin ziyarar ne domin tattaunawa da jami’i mai kula da harkokin Syria da kuma mataimakin ministan harkokin waje.

Shaibani ya kuma kara da cewa; kasashen Iran da Rasha suna da mastaya iri daya akan batutuwa mabanbanta  da su ka shafi Syria,kuma a yayin wannan ziyarar sun cimma matsaya akan ci gaba da tattaunawa da yin shawarwari a tsakaninsu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Shaibani ya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki

Iran ta yi Allah wadai da Kwamitin Sulhun na MDD na rashin tabaka komai wajen  dakatar da ayyukan Amurka da Isra’ila wanda Iran din ta bayyana da abin kunya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya yi tir da munanan hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Yemen da kuma yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kai wa Falasdinawa hari a zirin Gaza, tare da yin Allah wadai da rashin daukar wami mataki daga kwamitin sulhu na fuskantar wadannan munanan ayyukan.

Esmaeil Baghaei, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana matukar na dama kan yadda ake kashe fararen hula da suka hada da mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata muhimman ababen more rayuwa na kasar Yemen, sakamakon hare-haren da Amurka ke kaiwa.

Ya bayyana hare-haren da Amurka ta kai ta sama a matsayin laifukan yaki da laifukan ta’addanci, yana mai danganta hakan da “abin kunya da rashin gaskiya” na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da sauran cibiyoyin kasa da kasa kan wannan ta’asa.

Ya ce Amurka da gwamnatin yahudawan sahyoniya sun kitsa wani shiri na hadin gwiwa na raunana al’ummar musulmi da kuma rufe duk wata muryar goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta.

Daga karshe Baghaei ya jaddada nauyin da ya rataya a wuyan kasashen musulmi na duniya na dakatar da zaluncin da Isra’ila ke yi da kuma hare-haren da sojojin Amurka suke yi a kan Falasdinawa da sauran al’ummar musulmi, yana mai kira ga gwamnatocin musulmi da su dauki matakin da ya dace da kuma kokarin da kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ke yi na shawo kan lamarin.

Akalla Falasdinawa 436 da suka hada da kananan yara 183 ne aka kashe tun bayan da Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza a ranar Talata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • Kotun Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki
  • ‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’
  • Iran Ta Kira Jakadun Kasashen Jamus da Butaniya Zuwa Ma’aikatar Harkokin Waje Don Jan Kunnensu
  • A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya
  • MDD Ta Zargi Kasar Rasha Da Aikata Laifukan Yaki A Ukraine
  • Trump, ya ce ya yi tattauna mai armashi da Zelensky, bayan wacce ya yi da Putin