Iran Ta Sanar Da Samun Sakwanni Daga Mahukuntan Syria
Published: 15th, February 2025 GMT
Babban jami’i mai kula da harkokin Syria a ma’aikatar harkokin wajen Iran, Muhammad Ridha Ra’uf Shaibani ya sanar da cewa, sun yi musayar sakwanni da kasar Syria, kuma sun bude kafar ttataunawa ta kai tsaye.
Ra’uf Shaibani wanda ya kai ziyara kasar Rasha domin ttataunawa da mahukuntan kasar, ya fada a jiya Juma’a da marece cewa, Muna cikin shiri da tanadin sake dawo da alaka da kasar Syria anan gaba.
Har ila yau. Shaibani ya ce; Muna bin diddigin abubuwan da suke faruwa a Syria, kuma za mu dauki matsaya a lokacin da ya dace.”
Haka nan kuma ya ce; Muna kallon Syria ne a matsayin kasa wacce take da matsayi a cikin yankin yammacin Asiya, kuma mun yi imani da cewa, al’ummar kasar ne za su ayyana makomarta, don haka ya zama wajibi dukkanin bangarorin siyasar da ake da su a kasar su shiga ayi da su.”
Dangane da ziyarar da ya kai kasar Rasha, Shaibani ya ce; yana yin ziyarar ne domin tattaunawa da jami’i mai kula da harkokin Syria da kuma mataimakin ministan harkokin waje.
Shaibani ya kuma kara da cewa; kasashen Iran da Rasha suna da mastaya iri daya akan batutuwa mabanbanta da su ka shafi Syria,kuma a yayin wannan ziyarar sun cimma matsaya akan ci gaba da tattaunawa da yin shawarwari a tsakaninsu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shaibani ya
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
Ministan Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadaccen Abinci, Sanata Abubakar Kayri ne ya bayyana a haka, a cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar.
“Mun samar da tsarin samar da wadataccen abinci a kasar nan, wanda kowanne dan kasar zai amfana da shi”, in ji Kyari.
Daga cikin manyan abubuwan da suka hada da bashin sun hada da; samar da ingantaccen Irin Shinkafa da kuma habaka yadda ake samar da Irin na Shinkafar.
Sauran sun hada da mayar da hankali wajen yin girbin mai kyau, samar da nau’ikan Shinkafar da ke jurewa kowacce irin cutar da ke lalata Irin Shinkafar da aka shuka, aka ajiye a cibiyar gudanar da bincike kan amfanin gona (NCRI) da ke yankin Badeggi a Jihar Neja.
Kazalika, akwai kuma bukatar kara bunkasa kayan aikin gona, inganata aikin malaman gona, amfani da kayan aikin gona na kimiyya domin rika samar da bayanai a kan lokaci, musamman wanda ya shafi sauyin yanayi, samar da farashin kayan amfanin gona a kasuwa, dakile barkewar kwarin da ke lalata amfanin gona da sauransu.
A nasa jawabin, Karamin Minista a Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Dakta Abdullahi Sabi Abdullahi, ya bayyana gamsuwar da cewa, shuka ingantaccen Irin noma zai taimaka wajen ciyar da daukacin ‘yan Nijeriya gaba.
Dakta Abudullahi ya kara da cewa, ingantancen Iri shi ne, kashin bayan da zai kawo karshen kalubalen da bangeren samar da wadataccen abinci a kasar.
“Wannan hadaka za ta kara karfafawa, musamman kananan manoma na kasar nan guiwa, ta hanyar yin amfani da aikin karfafa wa kanannan manoma gwiwa, wato SHEP, wanda a yanzu aikin ya karade jihohi 14 na kasar nan”, a cewar Abdullahi.
Kazalika, wannan hadakar ta kasance tamkar cike wani gibi ne a tsakanin gudanar da bincike, yin aiki a aikace tare kuma da samar wa manoman kasar nan kayan aikin gona na zamani da kuma samar musu da ilimin kwarewar da ya kamata a fannin na aikin noma.
Shi kuwa, Darakta Janar na Hukumar, wanda kuma shi ne har ila yau, ya jagoranci tawagar kasar ta Japan, Takao Shimokawa ya bayyana cewa, Hukumar ta JICA da kuma Kasar Japan, sun mayar da hankali wajen ganin an bunkasa bangaren noman Shinkafa a Afirka, musamman ma a Nijeriya, duba da cewa, kasar ta kasance kan gaba wajen noman Shinkafa.
Wannan shirin ya nuna a zahiri irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya da Hukumar JICA suka yi, don kara habaka bangaren samar da wadataccen abinci a kasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp