Amincewa da Karin kudin dai ya zo ne domin cike gibin da aka samu, bayan da Amurka ta yanke kudaden taimakon da take bayarwa a fagen kiwon lafiya.

A shekarar 2023 Kasar Najeriya mai mutane fiye da miliyan 200 tana cikin 10 na farko da su ka fi karbar tallafin hukumar Amurka na raya kasashe ( USAID). Sai dai a halin yanzu shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dakatar da wannan taimakon  na tsawon kwanaki 90.

Wani dan majalisar dattijan Najeriya Sen. Adeola Olamkilekan wanda ya yi Magana a yayin zaman majalisar na amincewa da Karin kasafin kudin ya ce; Kasar ta za ji jiki sosai saboda yadda Amurka ta yanke tallafin, musamman a fagen dakile cutuka.

Dala miliyan 200 da aka amince da su, suna cikin kasafin kudin kasar ne na dala biliyan 36.6.

Za a yi amfani da mafi yawancin kudaden ne dai domin samar da magungunan riga-kafi da kuma magance cututtuka na annoba.

A shekarar 2023 Amerika ta bai wa Najeirya dala miliyan 600, domin amfani da su a fagen kiwon lafiya. Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya ce, an bayar da wadancan kudaden ne dai domin riga-kafin zazzabin Malariya, da kuma rika-kafin cutar HIV da magungunanta.

Bugu da kari,  yanke taimakon na Amurka zai iya shafar fagen ayyukan jin kai, musamman a yankin Arewa maso gabashin kasar da ake fama da matsalar masu dauke da makamai dake kashe mutane tun 2009 da ya haddasa kwararar ‘yan gudun hijira masu yawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas

Majalisar Wakilai ta ƙaryata zargin da ake mata na karɓar cin hanci domin amincewa da dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana a Jihar Ribas.

Ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Gwaram a Jihar Jigawa, Hon. Yusuf Shittu Galambi, ya kare majalisar yayin da ake ta cece-kuce kan batun.

Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Wasu ƙungiyoyi na zargin majalisar da yin ƙasa a gwiwa wajen yanke hukunci kan lamarin.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Galambi, ya ce babu gaskiya a zargin da ake yi cewa an tursasa ’yan majalisa ko an ba su na goro don su amince da matakin shugaban ƙasa.

Ya bayyana cewa yawancin mambobin majalisar sun goyi bayan matakin ne domin kare dimokuraɗiyya da kuma tsare muradun al’ummar Jihar Ribas.

“Mun yanke shawarar ne bisa kishin ƙasa, haɗin kan siyasa, zaman lafiya, da kare dimokuraɗiyya,” in ji shi.

Ya ce ya yi mamakin yadda wasu kafafen yaɗa labarai ke baza jita-jita cewa an tilasta musu su amince da dokar ta-ɓaci tare da karɓar daloli.

A cewarsa, ya kamata ’yan Najeriya su fahimci cewa ’yan majalisa suna aiki ne don ganin an samar da tawagar sulhu kafin wa’adin dokar ta-ɓacin ta ƙare.

Ya jaddada cewa dole ne a kare dimokuraɗiyya a Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • Wike Ya Kwace Filaye 4,794 A Abuja Saboda Rashin Biyan Kudin Ka’ida
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS