Leadership News Hausa:
2025-03-23@03:21:32 GMT

Mummunan Hatsari Ya Kashe Mutane 23, Da Yawa Sun Jikkata A Kano

Published: 15th, February 2025 GMT

Mummunan Hatsari Ya Kashe Mutane 23, Da Yawa Sun Jikkata A Kano

Hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) reshen jihar Kano ta tabbatar da cewa mutane 23 ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin da ya afku a gadar sama ta Muhammadu Buhari da ke kan hanyar Kano zuwa Maiduguri a ranar Juma’a nan da ta gabata.

A cewar hukumar FRSC, hatsarin ya rutsa da wata tirela ce wacce take ɗauke da kayayyaki da fasinjoji.

Watanni 2 Da Sauke Baffa Bichi, An Nada Umar Farouk Mukamin Sakataren Gwamnatin Kano Gidaje Da Dabbobi Sun Ƙone A Yayin Da Gobara Ta Tashi A Wani Ƙauyen Kano

Binciken farko ya nuna cewa hatsarin ya faru ne sakamakon tukin ganganci wanda aka fi alakƙanta shi da faruwar lamarin. Hatsarin ya rutsa da a ƙalla mutane 71, inda 48 suka samu raunuka, yayin da 23 suka mutu.

Jami’an bayar da agajin gaggawa na FRSC tare da haɗin gwuiwa da rundunar ‘yansandan Nijeriya sun isa wurin da lamarin ya faru cikin gaggawa domin ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara

Dakarun Sashe na 2 tare da hadin gwiwar sojojin sama na rundunar hadin gwiwa ta Operation Fansan Yamma sun ceto mutane 101 da aka yi garkuwa da su a fadin Kankara a jihar Katsina da Shinkafi a jihar Zamfara a ranakun 17 da 18 ga watan Maris 2025.

 

A cewar sanarwar mai Magana da aywun rundunar Fansan Yamma, Laftanar Kanar Abubukar Abdullahi ya bayyana cewa, a yayin farmakin an kashe ‘yan ta’adda 10 a wata arangama da suka yi a gundumar Faru da ke karamar hukumar Maradun.

 

Ta ce an fara kai farmakin ne a jihar Katsina, inda sojoji suka kai farmakin a kan ‘yan ta’addan a babbar filin Pauwa da ke karamar hukumar Kankara.

 

“Hakan ya yi sanadin kashe ‘yan ta’adda 3 tare da ceto mutane 84 da aka yi garkuwa da su.

 

A halin da ake ciki kuma, a jihar Zamfara, sojojin sun aiwatar da wasu ayyuka a yankin Bagabuzu da ke gundumar Faru, cikin karamar hukumar Maradun wanda ya kai ga halaka ‘yan ta’adda 7 tare da kwato babur da dai sauransu.

 

Bugu da kari, an yi nasarar ceto mutane 17 da wani sarkin ‘yan ta’adda ya yi garkuwa da su daga kauyukan Tsibiri da Doka da ke karamar hukumar Shinkafi, kuma a halin yanzu suna samun kulawar likitoci a wani asibiti da ke yankin.

 

Sanarwar ta bayyana cewa, Operation Fansan Yamma na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron al’ummar jihohin Katsina da Zamfara.

 

REL/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bam ya kashe mutum 4 da jikkata wasu a Borno
  • Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri
  • ’Yan bindiga sun yi garkuwa da jami’in FRSC a Benuwe
  • Gaggan Masu Garkuwa Da Mutane 10 Da Kayan Aikinsu Sun Shiga Hannu A Kano
  • Mutane Fiye Da 30 Ne Suka Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Dawkar Gas Ta Yi Bindiga A Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara
  • Cutar Sankarau Ta Kashe Mutane 56 A Kebbi
  • Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja
  • Mutane Da Dama Ne Ake Jin Tsoron Sun Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Daukar Gas Ta Yi Bindiga A Kan Gadar Karu A Birnin Abuja