HausaTv:
2025-02-20@08:58:22 GMT

Kasashen Larabawa A MDD Sun Yi Watsi Da Shirin Trump Na Korar Falasdinwa Daga Gaza

Published: 15th, February 2025 GMT

Jakadun kasashen larabawa da kuma na wasu kasashen duniya sun bayyana rashin amincewarsu da shirin shugaban kasar Amurka Donal Trump na korar Falasdinawa daga yankin Zirin gaza, saun kuma bayyana hakan a matsayin wanda ya sabawa dokokin kasa da kasa.

Shirin Trump na korar Falasdinawa daga Gaza dai ya fusata kasashen duniya musamman kasashen larabawa da musulmi, sun kuma ki amincewa da duk wani abu da zai sauyawa Falasdinawa kasarsu.

Wannan yana faruwa ne bayan da HKI ta kasa kwace zirin Gazar a hannun mayakan Hamas da kawayenta na wasu kungiyoyi masu gwagwarmaya a yankin.

Amurka tana son abinda yahudawan basu same shi a yaki ba Trump ya zo ya kwace shi ya mika masu ba tare da wata wahala ba. Sun ki amincewa da hakanne don ya sabawa doka ta 49 na MDD ta shekara 1949, inji Al-Bannai wanda yake magana a madadin kasashen laraba.

Kungiyar kasashen larabawa dai sun ki amincewa da hakan sun kuma sami cikekken goyon bayan kungiyar OIC ta kasashen musulmi da kuma kungiyar yan ba ruwammu, wato ‘the Non-Aligned Movement’ (NAM).

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata

Bunkasar kasashen duniya na bai daya ya zama tabbas, wanda kuma yake tabbata. Kamar yadda shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya bayyana a wajen taron tsaro na Munich, “Kasashe daban daban na tabbatar da bunkasarsu yanzu a maimakon yadda muke a baya. A lokacin da aka kone tsoffin gadoji, ana gina sabbi…kuma ya kamata mu sake hada kasashen duniya bisa wadannan sabbin gadoji.” (Lubabatu)

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  •  Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • Kasashen Rasha Da Amurka Sun Kuduri Anniyar Kawo Karshen Yaki A Ukraine
  • Daga Munich Zuwa Addis Ababa, Ci Gaban Kasashe Daban Daban Na Tabbata
  • Hamas Ta Yabawa Tarayyar Afirka Kan Yin Tir Da Kisan Kare Dangin Isra’ila A Gaza
  • Iran: Himmati Yana Halattar Taro Dangane Da Matsalolin Da Suka Addabar Kasashe Masu Tasuwa
  • Trump Ya fadawa Turawa Kan Cewa Basa Cikin Tattaunawa Kan Tsagaita Wuta A Ukraine
  • Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau