Ministan Tattalin Arziki Na Kasar Iran Ya Kama Hanyar Kasar Saudiya Don Halattar Taron Tattalin Arziki
Published: 15th, February 2025 GMT
Ministan kudi da tattalin arziki na kasar Iran yana kan hanyarsa ta zuwa kasar Saudiya don halattar wani taro mai muhimmaci na tattalin arziki.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan tattalin yana fadar haka a shafinsa na X, ya kuma kara da cewa, yana zuwa wannan taron ne tare da gayyar tokwaransa na kasar Saudiya da kuma kum ashugaban hukumar lamuni ta duniya, wato IMF.
Abdulnaser Himmati ya bayyana cewa manufae taron itaa ce tattauna hanyoyin bukasa tattalin arzikin kasashe masu tasowa . Har’ila yau taron tana son kyuatata dangantakar tattalin arziki a kasashen yankin Asia da kuma aiki tare da sauran kasashen duniya sabota ci gaban kasashen duniya gaba daya.
Taron na kwanaki biyu, wata dam ace ga kasar Iran ta bunkasa dangantakarta da sauran kasashen duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Jagora ya yi kira da a karfafa dogaro da kai a cikin gida domin dakile tasirin takunkumai
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya taya al’ummar Iran murnar zagayowar lokacin bukukuwan Nowruz na sabuwar shekarar hijira shamsiyya da ake amfani da itya a hukumance a kasar Iran.
Ayatullah Khamenei ya bayyana hakan ne a wani sako da ya aikewa al’ummar kasar ta gidan telebijin na murnar shiga sabuwar shekara ta Farisa a yammacin wannan Alhamis.
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya jaddada bukatar gwamnati da al’ummar kasar su ci gaba da zuba jari don karfafa azamarsu wajen tunkarar takunkumai na zalunci da masu girman kai na duniya suka kakaba ma kasar.
Ayatullah Khamenei ya jaddada cewa samar da kayayyaki na samun bunkasuwa ne idan aka ba da tallafin jari mai karfi.
Jagoran ya kuma yi Allah wadai da sabbin hare-haren da Isra’ila da take kaiwa Gaza, inda ya yi kira ga kasashen duniya baki daya da su nuna adawa da laifukan da Amurka da Isra’ila ke aikatawa a Gaza.
A yayin da ya koma kan batun kasar Yemen, Ayatullah Khamenei ya bayyana hare-haren da Amurka ke kai wa al’ummar kasar Yemen a matsayin wani laifi da ya zama wajibi a dakatar da shi.
Ya bayyana fatan alheri, nasara, da alheri ga al’ummar musulmi a cikin sabuwar shekara.