Zaɓen Katsina: An Samu Ƙarancin Masu Kaɗa Ƙuri’a Da Zargin Sayen Ƙuri’u
Published: 15th, February 2025 GMT
Ana ci gaba da gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi a Jihar Katsina, inda ake fuskantar ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a, da kuma zargin sayen ƙuri’u a wasu rumfunan zabe.
Jami’an tsaro, ciki har da ‘yansanda da NSCDC, sun sanya dokar taƙaita zirga-zirga tare da tura jami’ai wurare masu muhimmanci domin tabbatar da tsaro.
A rumfar Birchi ta Kudu, inda aka yi rajistar masu zabe 808, kaɗan daga cikinsu ne suka bayyana, wasu kuma sun ce an basu ₦500 bayan sun kaɗa ƙuri’unsu. Duk da babu rahoton tashin hankali, ƙarancin fitowar masu zaɓe da zargin sayen ƙuri’u na ƙara haifar da shakku kan ingancin zaɓen.
কীওয়ার্ড: Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
‘Za a fara biyan Naira 77,000 ga masu yi wa ƙasa hidima daga Maris’
Masu yi wa ƙasa hidima (NYSC), za su fara jin daɗin sabon alawus ɗin gwamnatin tarayya na N77,000.00 wanda aka sake duba shi da za a fara biya daga watan Maris, 2025.
Babban Darakta Janar (DG) na NYSC, Birgediya Janar Olakunle Oluseye Nafiu ne ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga masu yi wa ƙasa hidima a babban birnin tarayya, a ofishin NYSC na shiyya ta 3 da ke Wuse Zone 3 Old Parade Ground a yankin Garki a ranar Alhamis.
Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati ’Yan Boko Haram 7 sun miƙa wuya ga sojojin MNJTF a BornoYa sanar da masu yi wa ƙasar hidima cewa ma’aikatar kuɗi ta sanar da Hukumar NYSC cewa an shirya kuɗaɗen alawus ɗin don fara biya.
Ya bayyana cewa jinkirin aiwatar da sabon alawus ɗin ya biyo bayan rattaba hannu ne kan kasafin kuɗi na shekarar 2025.
Yayin da yake yabawa mambobin NYSC bisa kiyaye manufofin shugabannin da suka kafa NYSC ta hanyar samar da haɗin kan ƙasa, haɗe kai da ci gaban ƙasa, shugaban NYSC ya roƙe su da su yi amfani da ma’anar yadda aka rubuta taken waƙen NYSC.