Gobara ta ƙone ofishin INEC a Sakkwato
Published: 15th, February 2025 GMT
Hukumar Zaɓe Mai ta Ƙasa (INEC) ta ce ofishinta na Ƙaramar hukumar Gwadabawa da ke Jihar Sakkwato ya ƙone ƙurmus, inda gobarar ta lalata akwatunan zaɓe da sauran kayayyaki.
Mista Sam Olumekun, kwamishinan Hukumar INEC kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a wata sanarwa.
A cewarsa, a taron Hukumar INEC na mako-mako da aka saba gudanarwa a ranar Alhamis, hukumar ta lura da wani mummunan lamari na tashin gobara a ofishin ƙaramar hukumar Gwadabawa da ke Jihar Sakkwato, kamar yadda sakatariyar gudanarwa mai kula da ofishin jihar, Hauwa Aliyu Kangiwa ta ruwaito.
Ya ce gobarar ta tashi ne da sanyin safiyar Talata 11 ga watan Fabrairun 2025.
“Duk ginin ofishin ya lalace. Kayayyakin da suka lalace sun haɗa da tebura da kujeru da kayan aiki da kayan zaɓe da ake iya ɗauka, daga cikinsu akwai akwatunan zaɓe 558, rumfar kaɗa ƙuri’a 186, jakunkuna 186 na zaɓe da kuma kayayyakin da suka haɗa da manyan tankunan ruwa guda 12 (litta 1,000), tabarmin barci 400 da bokitan robobi 300.
“Rahoto na farko daga ofishinmu na jihar ya nuna cewa an samu ƙaruwar wutar lantarki kafin faruwar lamarin,” in ji Olumekun.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
Kungiyoyin Falasdina mabanbanta sun yi kira da a gudanar da taron musamman na al’ummar Falasdinu domin a tattauna hanyoyin da za a dakile batun tilastawa mutanen Gaza yin hijira.
Kungiyoyin na falasdinawa sun bayyana hakan ne dai a wani taro da su ka yi a Gaza domin karfafa gwiwar mutanen wannan zirin su ci gaba da jajurcewa da tsayin dakar da suke yi, tare da kara da cewa; Babu yadda za a yi al’ummar Falasdinu su fita daga kasarsu.
Mahalarta taron na Gaza sun bayyana furucin da shugaban kasar Amurka ya yi akan fitar da Falasdinawa daga Gaza da cewa yana nuni akan yadda Amurka da ‘yan sahayoniya su ka yi tarayya a laifukan da aka tafka akan Falasdinawa, haka nan ita kanta wannan maganar tana nufin shelanta wani sabon yakin akan al’ummar Falasdinu da hakan yake da bukatar fitar da wani matsayin na kasashen larabawa da kuma kungiyoyin kasa da kasa.
A karshe sun bukaci ganin cewa taron kasashen larabawa da za a yi nan gaba kadan, ya fito da wani tsari na ci gaban al’umma, saboda kawo karshe duk wani batu na yin hijira. Haka nan kuma sun bukaci ganin masu alaka da ‘yan mamaya daga cikin larabawa sun yanke ta.
Jami’in da yake kula da tuntubar juna a tsakanin kungiyoyi mabanbanta Khalid al-Badhash ya bayyana cewa; Duk da baranazar da hakkokin falasdinawa suke fuskanta, da kuma makirece-makircen Amurka, sai dai kuma batun kare hakkokin Falasdinawa ya sake dawowa da karfi a duniya, kuma duniyar ta gane hakikanin ‘yan mamaya.