Rahoton ya ce an fara badakalar ne a ranar 10 ga watan Disamba a lokacin da kamfanin harhada magunguna ya samu sakon imel dake nuna wani mai sayar da shi, Accent Pharma, yana neman a biya shi wani sabon asusun ajiya na banki.

Ba tare da sanin sakon imel din na yaudara ne ba, ana zargin kamfanin harhada magunguna ya aika Rs 11.

76 lakh, kamar yadda PUNCH Metro ta fahimci.

Wakilinmu ya ruwaito cewa kamfanin ya gano cewa an yi kutse ne bayan an biya kudin da kuma tantancewa. Wannan ya haifar da kwakkwaran bincike daga sashin damfarar intanet na kasar.

Rahoton ya kara da cewa, “Masu bincike sun binciki email din da aka yi wa kutse zuwa Nijeriya inda suka bi diddigin kudaden a asusun bankin Manipur. Hotunan sa ido sun kai ga kama Ngomere.

“An same shi ba tare da ingantacciyar takardar biza ta Indiya ba kuma ana zarginsa da kasancewa wani babban jami’in kungiyar. An yi rajistar FIR a karkashin Bharatiya Nyaya Sanhita da Dokar Baki. Ana ci gaba da bincike.”

A watan Janairun 2025, jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa Babban Sashen Binciken Laifuka na Kuwait a Jihar Ahmadi ya kama wasu ‘yan Nijeriya biyu da laifin fashi da makami.

An kama wadanda ake zargin ne cikin sa’o’i 24 bayan sun yi fashi a ofishin musayar kudi a Mahboula, wansu gundumomi a kudancin birnin Kuwait.

Ana zargin sun saci kudaden kasashen waje da suka kai Dinar Kuwaiti 4,600, kwatankwacin Dalar Amurka kusan 14,918.69 dangane da kudin musaya na currencyconbertonline.com.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Damfara

এছাড়াও পড়ুন:

Dubban Mutane Sun Fito Zanga-Zangar Yin Allawadai Da Kama Magajin Garin Istambul

Dubban dubatan mutane masu goyon bayan magajin garin Istambul a kasar Turkiya ne suka fito kan titunan birnin inda suke bukatar gwamnatin Urdugan ta sake shi.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa mutane suna ganin Ekrem Imamoglu, dan takarar shugaban kasa ne a zaben shugaban kasa mai zuwa kuma mai yuwa ya kara shugaban Urdugan a zaben, saboda yawan magoya bayansa a kasar, musamman a birnin Istambul.

Labarin ya kara da cewa Imamoglu mutum ne wanda yake da karbuwa a cikin mutanen kasar, wanda kuma ana ganin mai yuwa ya kada shugaba Urdugan a zaben shugaban kasa mai zuwa. Don haka ana ganin gwamnatin Urdugan ta sa aka kamashi, tare da zargin cin hanci da rashawa, don bata sunansa.

Gwamnatin Urdugan ta yi amfani da Jami’an tsaro don murkushe zanga-zangar masu goyon bayan magajin garin a jiya Alhamis, saboda ya ci gaba da zama mutumin da aka fi son ya ci gaba da shugabancin kasar.

Banda haka gwamnatin Urdugan ta kama Imamoglu ne bayan koma bayan da jam’iyyarsa ta gamu da shi a wani zaben da aka yi a kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • ’Yan daba sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
  • Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba
  • ’Yan bindiga sun hallaka matashi ana sallar Tahajjud a Kaduna
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Taƙaddama: An kama wanda ya daɓa wa matarsa ​​wuƙa ta mutu
  • Dubban Mutane Sun Fito Zanga-Zangar Yin Allawadai Da Kama Magajin Garin Istambul
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • EFCC Ta Cafke Akanta-janar Na Jihar Bauchi Kan Zargin Badaƙalar Naira Biliyan 70