Rahoton ya ce an fara badakalar ne a ranar 10 ga watan Disamba a lokacin da kamfanin harhada magunguna ya samu sakon imel dake nuna wani mai sayar da shi, Accent Pharma, yana neman a biya shi wani sabon asusun ajiya na banki.

Ba tare da sanin sakon imel din na yaudara ne ba, ana zargin kamfanin harhada magunguna ya aika Rs 11.

76 lakh, kamar yadda PUNCH Metro ta fahimci.

Wakilinmu ya ruwaito cewa kamfanin ya gano cewa an yi kutse ne bayan an biya kudin da kuma tantancewa. Wannan ya haifar da kwakkwaran bincike daga sashin damfarar intanet na kasar.

Rahoton ya kara da cewa, “Masu bincike sun binciki email din da aka yi wa kutse zuwa Nijeriya inda suka bi diddigin kudaden a asusun bankin Manipur. Hotunan sa ido sun kai ga kama Ngomere.

“An same shi ba tare da ingantacciyar takardar biza ta Indiya ba kuma ana zarginsa da kasancewa wani babban jami’in kungiyar. An yi rajistar FIR a karkashin Bharatiya Nyaya Sanhita da Dokar Baki. Ana ci gaba da bincike.”

A watan Janairun 2025, jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa Babban Sashen Binciken Laifuka na Kuwait a Jihar Ahmadi ya kama wasu ‘yan Nijeriya biyu da laifin fashi da makami.

An kama wadanda ake zargin ne cikin sa’o’i 24 bayan sun yi fashi a ofishin musayar kudi a Mahboula, wansu gundumomi a kudancin birnin Kuwait.

Ana zargin sun saci kudaden kasashen waje da suka kai Dinar Kuwaiti 4,600, kwatankwacin Dalar Amurka kusan 14,918.69 dangane da kudin musaya na currencyconbertonline.com.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Damfara

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto

Wani rahoto da kwamitin bincike da Gwamnatin Jihar Kano ta kafa kan zanga-zangar yunwa, ya gano cewa mutum 10 sun rasa rayukansu, yayin da wasu mutum bakwai suka samu munanan raunuka.

Rahoton ya kuma bayyana cewa an yi asarar dukiya da ta kai Naira biliyan 11, sakamakon ƙone-ƙone, sace-sace, da lalata kadarorin gwamnati da na ’yan kasuwa a faɗin jihar.

Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram

Da yake jawabi a taron majalisar zartaswar ta jihar karo na 25 a ranar Talata, Gwamnan Jihar, Abba Kabir Yusuf, ya karɓi rahoton daga shugaban hannun kwamitin, Mai shari’a Lawan Wada (ritaya).

Ya tabbatar da cewa za a fitar da takarda a hukumanci don bayyana waɗanda suka ɗauki nauyin tashin hankali yayin zanga-zangar.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bsture Dawaki Tofa ya fitar, zanga-zangar ta yi sanadin rasuwar rayukan mutum 10, yayin da wasu bakwai duka samu munanan raunuka.

Hakazalika ya ce an yi asarar dukiya da ta kai Naira biliyan 11.

“Na gamsu da gaskiya da ƙwarewar mambobin kwamitin. An zaɓe su bisa cancanta, kuma ina da yaƙinin sun yi aikinsu ba tare da son rai ba,” in ji Gwamna Abba.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba ta tsoma baki a binciken da ya ɗauki watanni shida ana yi ba, domin bai wa kwamitin damar gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

“Gwamnati za ta ɗauki matakin da ya dace dangane da abubuwan da aka gano a cikin rahoton.

“Wannan zai zama izina ga masu tayar da tarzoma da haddasa ɓarna a jihar,” a cewarsa.

Da yake gabatar da rahoton, Mai shari’a Wada, ya bayyana cewa kwamitin ya ziyarci wuraren da abin ya shafa tare da tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin tattara bayanai kan tasirin zanga-zangar.

“Alƙawarin da gwamnan ya ɗauka na aiwatar da shawarwarin rahoton yana nuna matakin da za a ɗauka don tabbatar da adalci da daidaito a Jihar Kano,” in ji sanarwar.

Gwamna Abba ya yaba wa kwamitin bisa aikin da suka yi, kuma ya buƙace su da su kasance a shirye idan gwamnati ta sake neman su za su yi wani aiki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Rayuka 10 da dukiyar N11bn sun salwanta yayin zanga-zangar tsadar rayuwa a Kano
  • Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto
  • USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri
  • EFCC Ta Cika Hannu Da Mutane 15 Kan Zargin Zamba Ta Intanet A Abuja
  • Hajji 2025: Kamfanin Saudiyya zai maka Najeriya a Kotun Duniya
  • Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon
  • Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe